Home General Amurka ta musanta zargin ɗaukar nauyin ta’addancin Boko Haram a Najeriya

Amurka ta musanta zargin ɗaukar nauyin ta’addancin Boko Haram a Najeriya

Amurka ta musanta zargin da ke bayyanata a matsayin mai ɗaukar nauyin ayyukan ta’addancin ƙungiyar Boko Haram a Najeriya, ƙungiyar da ta shafe tsawon shekaru ta na ƙaddamar da jerin hare-hare tare da kashe dubunnan ɗaruruwan mutane da suka ƙunshi fararen hula da ɗimbin jami’an tsaro baya ga tagayyara miliyoyin jama’a a ƙasar ta yammacin Afrika.

Jakadan Amurkan a Najeriya, Richard M. Mills Jr. da ke kawar da wannan zargi gaban manema labarai jim kaɗan bayan wata ganawar sirri da ya yi tare da gwamnonin jihohin Najeriya 36 ya ce Amurka ba ta hannu a ƙungiyar Boko Haram, hasalima ta na taimakawa Najeriya don ganin ta kawar da matsalar.

Tun farko ɗan Majalisar Amurka na jam’iyyar Republican da ke wakiltar Pennsylvania Scott Perry ne ya yi iƙirarin cewa hukumar raya ƙasashe ta Amurka USAID ce ke ɗaukar nauyin ƙungiyoyin ta’addanci a ƙasashe ciki har da Boko Haram ta Najeriya.

A ƙoƙarinsa na kare manufar shugaba Donald Trump game da rushe hukumar USAID, Scott ya ce kaso mai yawa na kuɗin da ake tattarawa da sunan tallafi suna ƙarewa ne a hannun ƴan ta’adda irin ISIS da Al-Qaeda sai kuma boko haram kana ISIS Khorasan.

A cewar Mills Jr, babu wata hujja da ke nuna Amurka na goyon bayan ta’addanci a Najeriya, hasalima akwai tarin hujjoji da ke tabbatar da yadda ta ke taimakawa ƙasar wajen magance matsalolin tsaron da suka fabaibayeta.

Jakadan na Amurka a Najeriya ya ce idan Washington ta samu ko da ƙaramar hujja ce da ke nuna ana karkatar da kuɗaɗen tallafin USAID ko sauran ƙungiyoyi da hukumomin Amurka zuwa ayyukan ta’addanci, ko shakka babu za su jagoranci bincike da haɗin gwiwar Najeriya don hukunta masu hannu a badaƙalar.

Ƙungiyar ta’addancin ta Boko haram ta shafe tsawon shekaru aƙalla 15 a yankin arewa maso gabashin Najeriya da wasu sassa na Chadi da Nijar da Arewacin Kamaru da kuma Mali.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp