Home General Amurka ta musanta zargin ɗaukar nauyin ta’addancin Boko Haram a Najeriya

Amurka ta musanta zargin ɗaukar nauyin ta’addancin Boko Haram a Najeriya

Amurka ta musanta zargin da ke bayyanata a matsayin mai ɗaukar nauyin ayyukan ta’addancin ƙungiyar Boko Haram a Najeriya, ƙungiyar da ta shafe tsawon shekaru ta na ƙaddamar da jerin hare-hare tare da kashe dubunnan ɗaruruwan mutane da suka ƙunshi fararen hula da ɗimbin jami’an tsaro baya ga tagayyara miliyoyin jama’a a ƙasar ta yammacin Afrika.

Jakadan Amurkan a Najeriya, Richard M. Mills Jr. da ke kawar da wannan zargi gaban manema labarai jim kaɗan bayan wata ganawar sirri da ya yi tare da gwamnonin jihohin Najeriya 36 ya ce Amurka ba ta hannu a ƙungiyar Boko Haram, hasalima ta na taimakawa Najeriya don ganin ta kawar da matsalar.

Tun farko ɗan Majalisar Amurka na jam’iyyar Republican da ke wakiltar Pennsylvania Scott Perry ne ya yi iƙirarin cewa hukumar raya ƙasashe ta Amurka USAID ce ke ɗaukar nauyin ƙungiyoyin ta’addanci a ƙasashe ciki har da Boko Haram ta Najeriya.

A ƙoƙarinsa na kare manufar shugaba Donald Trump game da rushe hukumar USAID, Scott ya ce kaso mai yawa na kuɗin da ake tattarawa da sunan tallafi suna ƙarewa ne a hannun ƴan ta’adda irin ISIS da Al-Qaeda sai kuma boko haram kana ISIS Khorasan.

A cewar Mills Jr, babu wata hujja da ke nuna Amurka na goyon bayan ta’addanci a Najeriya, hasalima akwai tarin hujjoji da ke tabbatar da yadda ta ke taimakawa ƙasar wajen magance matsalolin tsaron da suka fabaibayeta.

Jakadan na Amurka a Najeriya ya ce idan Washington ta samu ko da ƙaramar hujja ce da ke nuna ana karkatar da kuɗaɗen tallafin USAID ko sauran ƙungiyoyi da hukumomin Amurka zuwa ayyukan ta’addanci, ko shakka babu za su jagoranci bincike da haɗin gwiwar Najeriya don hukunta masu hannu a badaƙalar.

Ƙungiyar ta’addancin ta Boko haram ta shafe tsawon shekaru aƙalla 15 a yankin arewa maso gabashin Najeriya da wasu sassa na Chadi da Nijar da Arewacin Kamaru da kuma Mali.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp