Home General Amurka ta musanta zargin ɗaukar nauyin ta’addancin Boko Haram a Najeriya

Amurka ta musanta zargin ɗaukar nauyin ta’addancin Boko Haram a Najeriya

Amurka ta musanta zargin da ke bayyanata a matsayin mai ɗaukar nauyin ayyukan ta’addancin ƙungiyar Boko Haram a Najeriya, ƙungiyar da ta shafe tsawon shekaru ta na ƙaddamar da jerin hare-hare tare da kashe dubunnan ɗaruruwan mutane da suka ƙunshi fararen hula da ɗimbin jami’an tsaro baya ga tagayyara miliyoyin jama’a a ƙasar ta yammacin Afrika.

Jakadan Amurkan a Najeriya, Richard M. Mills Jr. da ke kawar da wannan zargi gaban manema labarai jim kaɗan bayan wata ganawar sirri da ya yi tare da gwamnonin jihohin Najeriya 36 ya ce Amurka ba ta hannu a ƙungiyar Boko Haram, hasalima ta na taimakawa Najeriya don ganin ta kawar da matsalar.

Tun farko ɗan Majalisar Amurka na jam’iyyar Republican da ke wakiltar Pennsylvania Scott Perry ne ya yi iƙirarin cewa hukumar raya ƙasashe ta Amurka USAID ce ke ɗaukar nauyin ƙungiyoyin ta’addanci a ƙasashe ciki har da Boko Haram ta Najeriya.

A ƙoƙarinsa na kare manufar shugaba Donald Trump game da rushe hukumar USAID, Scott ya ce kaso mai yawa na kuɗin da ake tattarawa da sunan tallafi suna ƙarewa ne a hannun ƴan ta’adda irin ISIS da Al-Qaeda sai kuma boko haram kana ISIS Khorasan.

A cewar Mills Jr, babu wata hujja da ke nuna Amurka na goyon bayan ta’addanci a Najeriya, hasalima akwai tarin hujjoji da ke tabbatar da yadda ta ke taimakawa ƙasar wajen magance matsalolin tsaron da suka fabaibayeta.

Jakadan na Amurka a Najeriya ya ce idan Washington ta samu ko da ƙaramar hujja ce da ke nuna ana karkatar da kuɗaɗen tallafin USAID ko sauran ƙungiyoyi da hukumomin Amurka zuwa ayyukan ta’addanci, ko shakka babu za su jagoranci bincike da haɗin gwiwar Najeriya don hukunta masu hannu a badaƙalar.

Ƙungiyar ta’addancin ta Boko haram ta shafe tsawon shekaru aƙalla 15 a yankin arewa maso gabashin Najeriya da wasu sassa na Chadi da Nijar da Arewacin Kamaru da kuma Mali.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp