Home General Najeriya da China sun cimma yarjejeniyar Yuro biliyan 7 a bangaren makamashi

Najeriya da China sun cimma yarjejeniyar Yuro biliyan 7 a bangaren makamashi

Najeriya da China sun rattaba hannu akan yarjejeniyar samar da makamashi mara gurɓata muhalli da ya kai Yuro biliyan 7 da miliyan ɗari 6 da zummar sauyawa daga amfani da makamashi mai gurɓata muhalli daidai da yadda dokokin duniya suka tanada.

A ƙarshen makon da ya gabata ne aka tabbatar da wannan yarjejeniya a hukumance a Uyo, babban birnin jihar Akwa Ibom a  tsakanin gwamnatin Najeriya da kamfanin  APPL Hydrogen Limited (AHL), da LONGi Green Energy Technology Company Limited  na ƙasar China.

Za a gudanar da wannan aiki ne yankin da aka sakar wa yan kasuwa mara su gudanar da sabgoginsu, wato Liberty Free Trade Zone da ke garin Atabrikang a ƙaraamar hukumar  Ibeno ta jihar Akwa Ibom.

Kamfanin LONGi, wanda ke kan gaba a hakar sauyawa zuwa amfani da makamashi mara gurɓata muhalli a duniya, da AHL na Najeriya, wanda ya ƙware wajen samar da makamashi da ba ya illata muhalli ne za su yi haɗaka don tafiyar da aikin, kamar yadda yake a cikin yarjejeniyar fahimtar juna da aka yi.

Da yake jawabi a yayin rattaba  hannu a yarjejeniyar, ministan kimiyya da fasaha na Najeriya, Uche Nnaji ya jaddada mahimmancin shirin a koƙarin da Najeriya ke yi wajen sauyawa zuwa amgfani da makamashin da ba ya illa ga muhalli.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp