Home General Najeriya da China sun cimma yarjejeniyar Yuro biliyan 7 a bangaren makamashi

Najeriya da China sun cimma yarjejeniyar Yuro biliyan 7 a bangaren makamashi

Najeriya da China sun rattaba hannu akan yarjejeniyar samar da makamashi mara gurɓata muhalli da ya kai Yuro biliyan 7 da miliyan ɗari 6 da zummar sauyawa daga amfani da makamashi mai gurɓata muhalli daidai da yadda dokokin duniya suka tanada.

A ƙarshen makon da ya gabata ne aka tabbatar da wannan yarjejeniya a hukumance a Uyo, babban birnin jihar Akwa Ibom a  tsakanin gwamnatin Najeriya da kamfanin  APPL Hydrogen Limited (AHL), da LONGi Green Energy Technology Company Limited  na ƙasar China.

Za a gudanar da wannan aiki ne yankin da aka sakar wa yan kasuwa mara su gudanar da sabgoginsu, wato Liberty Free Trade Zone da ke garin Atabrikang a ƙaraamar hukumar  Ibeno ta jihar Akwa Ibom.

Kamfanin LONGi, wanda ke kan gaba a hakar sauyawa zuwa amfani da makamashi mara gurɓata muhalli a duniya, da AHL na Najeriya, wanda ya ƙware wajen samar da makamashi da ba ya illata muhalli ne za su yi haɗaka don tafiyar da aikin, kamar yadda yake a cikin yarjejeniyar fahimtar juna da aka yi.

Da yake jawabi a yayin rattaba  hannu a yarjejeniyar, ministan kimiyya da fasaha na Najeriya, Uche Nnaji ya jaddada mahimmancin shirin a koƙarin da Najeriya ke yi wajen sauyawa zuwa amgfani da makamashin da ba ya illa ga muhalli.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp