Home General NNPP ta dakatar da jiga-jiganta hudu a Kano

NNPP ta dakatar da jiga-jiganta hudu a Kano

Jam’iyyar NNPP reshen Kano ta dakatar da wasu manyan mambobin ta hudu da suka hada da Sanata Kawu Sumaila, Ali Madakin Gini, Sani Abdullahi Rogo, da Kabiru Alhassan Rurum, bisa zarginsu da yiwa jam’iyyar zagon kasa.

Shugaban jam’iyyar na jihar Kano Hashimu Suleiman Dungurawa ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano.

Dungurawa yqace an zabi wadannan ‘yan majalisar dokokin ne a karkashin jam’iyyar NNPP amma a kwanakin baya suna yin wasu abubuwa da suka saba da Manufofi da akidar jam’iyyar.
Ya ce an ba su tikitin takara a jam’iyyar gabanin zabukan da suka gabata, amma maimakon su nuna godiya, sai suke yin abubuwan da suka ci karo da muradun jam’iyyar.

Wani lamari na baya-bayan nan da ya janyo dakatarwar shi ne yadda aka gudanar da daurin auren diyar Sanata Kawu Sumaila da kuma bikin yaye ɗaliban jami’ar kawu Sumaila.

Dungurawa ya bayyana mamakinsa da cewa wadanda suka halarci taron galibinsu mutane ne da su ka yaki Kawu a baya, amma kuma ya gayyatosu harkarsa kuma ya ki gayyatar ‘yan jam’iyya NNPP.

Shugaban jam’iyyar ya bayyana cewa za a kafa kwamitin da zai binciki lamarin tare da sanar da al’umma sakamakon karshe da jam’iyyar za ta dauka.

Duk da dakatarwar, Dungurawa ya jaddada cewa har yanzu akwai sauran damar tattaunawa ga wadanda aka dakatar din, idan har suka nemi afuwa jam’iyyar za ta iya yafe musu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp