Home General NNPP ta dakatar da jiga-jiganta hudu a Kano

NNPP ta dakatar da jiga-jiganta hudu a Kano

Jam’iyyar NNPP reshen Kano ta dakatar da wasu manyan mambobin ta hudu da suka hada da Sanata Kawu Sumaila, Ali Madakin Gini, Sani Abdullahi Rogo, da Kabiru Alhassan Rurum, bisa zarginsu da yiwa jam’iyyar zagon kasa.

Shugaban jam’iyyar na jihar Kano Hashimu Suleiman Dungurawa ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano.

Dungurawa yqace an zabi wadannan ‘yan majalisar dokokin ne a karkashin jam’iyyar NNPP amma a kwanakin baya suna yin wasu abubuwa da suka saba da Manufofi da akidar jam’iyyar.
Ya ce an ba su tikitin takara a jam’iyyar gabanin zabukan da suka gabata, amma maimakon su nuna godiya, sai suke yin abubuwan da suka ci karo da muradun jam’iyyar.

Wani lamari na baya-bayan nan da ya janyo dakatarwar shi ne yadda aka gudanar da daurin auren diyar Sanata Kawu Sumaila da kuma bikin yaye ɗaliban jami’ar kawu Sumaila.

Dungurawa ya bayyana mamakinsa da cewa wadanda suka halarci taron galibinsu mutane ne da su ka yaki Kawu a baya, amma kuma ya gayyatosu harkarsa kuma ya ki gayyatar ‘yan jam’iyya NNPP.

Shugaban jam’iyyar ya bayyana cewa za a kafa kwamitin da zai binciki lamarin tare da sanar da al’umma sakamakon karshe da jam’iyyar za ta dauka.

Duk da dakatarwar, Dungurawa ya jaddada cewa har yanzu akwai sauran damar tattaunawa ga wadanda aka dakatar din, idan har suka nemi afuwa jam’iyyar za ta iya yafe musu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp