Home General Gwamnatin Kano Ta Sanar Da Ranar Hutun Makarantun Firamare Da Sakandiren Jihar

Gwamnatin Kano Ta Sanar Da Ranar Hutun Makarantun Firamare Da Sakandiren Jihar

Gwamnatin jihar Kano ta amince da ranar juma’a 28 ga watan Fabrairun 2025, a matsayin ranar hutun Zango karatu na biyu ga makarantun firamare da sakandire dake faɗin jihar.

Ma’aikatar ilimi ta jihar Kano ce ta sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da daraktan wayar da kan al’umma na ma’aikatar Balarabe Abdullahi Kiru ya rabawa manema labarai, inda ya ce hutun ya shafi makarantu masu zaman kansu da kuma na gwamnati.

Sanarwar ta ce daliban makarantun firamare da sakandire na kwana za su koma Makarantunsu a ranar lahadi 06 ga watan Afirilun 2025, a yayin da su kuma na makarantun jeka ka dawo za su koma Makarantar a ranar litinin 07 ga watan Afirilu, 2025.

Kwamishinan ilimi na jihar Kano Dakta Ali Haruna Makoda, ya buƙaci iyayen yaran da su tabbatar da cewa ‘ya’yansu sun koma Makarantar a ranakun da aka sanya.

A ƙarshe sanarwar ta gargaɗi dukkan makarantu masu zaman kansu da su tabbatar da bin ƙa’idar da aka gindaya ko kuma su fuskanci hukunci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp