Home General Rundunar ‘Yan sandan Nijeriya ta janye Gayyatar da ta yiwa Sarkin Kano

Rundunar ‘Yan sandan Nijeriya ta janye Gayyatar da ta yiwa Sarkin Kano

Sifeto janar na ‘yansandan Najeriya ya janye gayyatar da hukumar ta yiwa Sarkin Kano Sanusi zuwa shelkwatar hukumar domin amsa tamabayoyi.

Umarnin janyewar ya fito ne ta baki mai magana da yawun hukumar Olumuyiwa Adejobi, inda ya ce janyewar ta zama wajibi bayan tsoma bakin da masu ruwa da tsaki suka yi a kasar, yana mai cewa hakan yayi daidai da tsarin aikinsu na tabbatar da aiyukansu ba a siyasantar dasu ko fahimtarsu a baibai ba.

Saidai sanarwar ta umarci kwamishinan ‘yansandan jihar da ya karbi bayanan binciken sarkin a jiharsa ta Kano.

Tun da fari dai rundunar ‘yan sandan ta kasa ta gayyaci Khalifa Muhammadu Sanusi ne bisa zargin karya dokar da ta saka na haramta yin dukkan wani hawa a cikin bukukuwan sallah Karama.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp