Home General Ƴanbindiga sun kashe ƴan sa-kai 13 a jihar Kebbi

Ƴanbindiga sun kashe ƴan sa-kai 13 a jihar Kebbi

Rahotanni daga jihar Kebbi a arewa maso yammacin Najeriya na cewa kimanin mutum 20 ne suka rasa rayukansu a wasu hare-hare da wasu ƴan bindiga suka kai a wasu garuruwa biyu a jiya Lahadi.

Lamarin ya faru ne a yankin karamar Hukumar Augie – ɗaya daga cikin yankunan da ake cewa mayaƙan Lakurawa na da sansani.

Koda yake kawo yanzu ba a tabbatar ko su wa ne maharan ba.

Wani ɗan jarida Jameel Gulma dake a yankin ya bibiyi labarin, inda ya ce maharan sun kashe mutum shida ne, suka kwashe shanu, sai ƴan sa-kai suka bi su.

“A nan suka yi wa ƴan sa-kan kwantan ɓauna, suka buɗe musu wuta, inda suka kashe guda 13 daga cikinsu.”

jihar ta Kebbi  na guda cikin jihohin arewacin Nijeriya dake fama da matsalar rashin tsaro, musamman na ‘yan bindiga dake satar mutane domin karbar kudin fansa wanda ke sake jifa jihar cikin halin na durkushewar tattalin arziki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp