Home General Gwamnoni 20 a Najeriya sun ƙi biyan mafi ƙarancin albashin dubu 70,000

Gwamnoni 20 a Najeriya sun ƙi biyan mafi ƙarancin albashin dubu 70,000

Shugaban ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi ta Najeriya ALGON Alhaji Haruna Ƙanƙara, yace har yanzu akwai jihohi 20 a ƙasar da basu fara biyan sabon tsarin mafi ƙarancin albashi na naira dubu 70 ga ma’aiktan ƙananan hukumomi da malaman makarantun firamare ba.

Shugaban ya ce jihohin sun haɗa da Yobe da Gombe da Zamfara da Kaduna da Imo da Ebonyi da Cross River da Abuja fadar gwamnatin ƙasar da Borno da sauransu.

Shugaban na NULGE ya yi wannan bayani ne a yayin wata zantawa da ya yi da jaridar Punch ta Najeriya, tare da ba da hankali akan biyan mafi ƙarancin albashin a ɓangaren ma’aikatan ƙananan hukumomi da Malaman Makarantun firamare.

Shugaban na Najeriya ya rattaɓa hanu kan ƙudirin dokar biyan naira dubu 70,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi ga ma’aikatan ƙasar ne a ranar 29 ga watan Yulin shekarar 2024, bayan wata yarjejeniya da suka cimma da jagororin ƙungiyar kwadago ta ƙasar.

An kara sabon mafi karancin albashin ne da kashi 133 wato daga N30,000 zuwa N70,000, a daidai lokacin da kasar ke fama da tabarbarewar tattalin arziki.

Da yake bayani kan yadda ake aiwatar da dokar, Kankara ya ce, “A gaskiya muna fuskantar kalubale a jihohi da dama, kamar kimanin 20 da har yanzu basu fara aiwatar da sabon mafi karancin albashi ba.

Ƙanƙara ya ci gaba da cewa ”akwai jihohi kamar Sokoto da Yobe da Gombe da da Zamfara da Kaduna da Imo da Ebonyi da Borno da Cross River da Abuja fadar gwamnatin ƙasar da sauran su, a yayin da wasunsu sun fara biyan sabon tsarin a mataki na jiha sai kuma suka yi watsi da na ƙananan hukumomi da Malaman makarantu, amma muna cigaba da fafutukar ganin an yiwa ma’aikatan adalci”.

Shugaban ya ƙara da cewa “wani ɓangare kuma wasu daga cikin gwamnonin sun alƙawarta cewa zasu biya amma suka gagara biya, sai dai muna iya ƙoƙarin ganin an shawo kan wannan matsalar”

Sannan dangane da batun aiwatar da ‘yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi kuwa, shugaban NULGE ya bayyana cewa har yanzu babban bankin kasar bai tattauna da majalisun ba kan bude asusun ajiyar banki.

“Abin da kungiyar ta ke bukata a koda-yaushe shi ne babban bankin Najeriya ya fitar da wani tsari ga kananan hukumomi da zai basu damar bude asusun ajiya da su, amma har yanzu ba a samu hakan ba”.

Sai dai Shugaban NULGE na jihar Kwara, Seun Oyinlade, ya ce gwamnatin jihar sa ta fara biyan Naira 70,000 ga ma’aikatan jihar tun a watan Oktoban shekarar 2024.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp