Home General Gwamnoni 20 a Najeriya sun ƙi biyan mafi ƙarancin albashin dubu 70,000

Gwamnoni 20 a Najeriya sun ƙi biyan mafi ƙarancin albashin dubu 70,000

Shugaban ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi ta Najeriya ALGON Alhaji Haruna Ƙanƙara, yace har yanzu akwai jihohi 20 a ƙasar da basu fara biyan sabon tsarin mafi ƙarancin albashi na naira dubu 70 ga ma’aiktan ƙananan hukumomi da malaman makarantun firamare ba.

Shugaban ya ce jihohin sun haɗa da Yobe da Gombe da Zamfara da Kaduna da Imo da Ebonyi da Cross River da Abuja fadar gwamnatin ƙasar da Borno da sauransu.

Shugaban na NULGE ya yi wannan bayani ne a yayin wata zantawa da ya yi da jaridar Punch ta Najeriya, tare da ba da hankali akan biyan mafi ƙarancin albashin a ɓangaren ma’aikatan ƙananan hukumomi da Malaman Makarantun firamare.

Shugaban na Najeriya ya rattaɓa hanu kan ƙudirin dokar biyan naira dubu 70,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi ga ma’aikatan ƙasar ne a ranar 29 ga watan Yulin shekarar 2024, bayan wata yarjejeniya da suka cimma da jagororin ƙungiyar kwadago ta ƙasar.

An kara sabon mafi karancin albashin ne da kashi 133 wato daga N30,000 zuwa N70,000, a daidai lokacin da kasar ke fama da tabarbarewar tattalin arziki.

Da yake bayani kan yadda ake aiwatar da dokar, Kankara ya ce, “A gaskiya muna fuskantar kalubale a jihohi da dama, kamar kimanin 20 da har yanzu basu fara aiwatar da sabon mafi karancin albashi ba.

Ƙanƙara ya ci gaba da cewa ”akwai jihohi kamar Sokoto da Yobe da Gombe da da Zamfara da Kaduna da Imo da Ebonyi da Borno da Cross River da Abuja fadar gwamnatin ƙasar da sauran su, a yayin da wasunsu sun fara biyan sabon tsarin a mataki na jiha sai kuma suka yi watsi da na ƙananan hukumomi da Malaman makarantu, amma muna cigaba da fafutukar ganin an yiwa ma’aikatan adalci”.

Shugaban ya ƙara da cewa “wani ɓangare kuma wasu daga cikin gwamnonin sun alƙawarta cewa zasu biya amma suka gagara biya, sai dai muna iya ƙoƙarin ganin an shawo kan wannan matsalar”

Sannan dangane da batun aiwatar da ‘yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi kuwa, shugaban NULGE ya bayyana cewa har yanzu babban bankin kasar bai tattauna da majalisun ba kan bude asusun ajiyar banki.

“Abin da kungiyar ta ke bukata a koda-yaushe shi ne babban bankin Najeriya ya fitar da wani tsari ga kananan hukumomi da zai basu damar bude asusun ajiya da su, amma har yanzu ba a samu hakan ba”.

Sai dai Shugaban NULGE na jihar Kwara, Seun Oyinlade, ya ce gwamnatin jihar sa ta fara biyan Naira 70,000 ga ma’aikatan jihar tun a watan Oktoban shekarar 2024.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp