Home General Gwamnoni 20 a Najeriya sun ƙi biyan mafi ƙarancin albashin dubu 70,000

Gwamnoni 20 a Najeriya sun ƙi biyan mafi ƙarancin albashin dubu 70,000

Shugaban ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi ta Najeriya ALGON Alhaji Haruna Ƙanƙara, yace har yanzu akwai jihohi 20 a ƙasar da basu fara biyan sabon tsarin mafi ƙarancin albashi na naira dubu 70 ga ma’aiktan ƙananan hukumomi da malaman makarantun firamare ba.

Shugaban ya ce jihohin sun haɗa da Yobe da Gombe da Zamfara da Kaduna da Imo da Ebonyi da Cross River da Abuja fadar gwamnatin ƙasar da Borno da sauransu.

Shugaban na NULGE ya yi wannan bayani ne a yayin wata zantawa da ya yi da jaridar Punch ta Najeriya, tare da ba da hankali akan biyan mafi ƙarancin albashin a ɓangaren ma’aikatan ƙananan hukumomi da Malaman Makarantun firamare.

Shugaban na Najeriya ya rattaɓa hanu kan ƙudirin dokar biyan naira dubu 70,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi ga ma’aikatan ƙasar ne a ranar 29 ga watan Yulin shekarar 2024, bayan wata yarjejeniya da suka cimma da jagororin ƙungiyar kwadago ta ƙasar.

An kara sabon mafi karancin albashin ne da kashi 133 wato daga N30,000 zuwa N70,000, a daidai lokacin da kasar ke fama da tabarbarewar tattalin arziki.

Da yake bayani kan yadda ake aiwatar da dokar, Kankara ya ce, “A gaskiya muna fuskantar kalubale a jihohi da dama, kamar kimanin 20 da har yanzu basu fara aiwatar da sabon mafi karancin albashi ba.

Ƙanƙara ya ci gaba da cewa ”akwai jihohi kamar Sokoto da Yobe da Gombe da da Zamfara da Kaduna da Imo da Ebonyi da Borno da Cross River da Abuja fadar gwamnatin ƙasar da sauran su, a yayin da wasunsu sun fara biyan sabon tsarin a mataki na jiha sai kuma suka yi watsi da na ƙananan hukumomi da Malaman makarantu, amma muna cigaba da fafutukar ganin an yiwa ma’aikatan adalci”.

Shugaban ya ƙara da cewa “wani ɓangare kuma wasu daga cikin gwamnonin sun alƙawarta cewa zasu biya amma suka gagara biya, sai dai muna iya ƙoƙarin ganin an shawo kan wannan matsalar”

Sannan dangane da batun aiwatar da ‘yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi kuwa, shugaban NULGE ya bayyana cewa har yanzu babban bankin kasar bai tattauna da majalisun ba kan bude asusun ajiyar banki.

“Abin da kungiyar ta ke bukata a koda-yaushe shi ne babban bankin Najeriya ya fitar da wani tsari ga kananan hukumomi da zai basu damar bude asusun ajiya da su, amma har yanzu ba a samu hakan ba”.

Sai dai Shugaban NULGE na jihar Kwara, Seun Oyinlade, ya ce gwamnatin jihar sa ta fara biyan Naira 70,000 ga ma’aikatan jihar tun a watan Oktoban shekarar 2024.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp