Home General Gwamnoni 20 a Najeriya sun ƙi biyan mafi ƙarancin albashin dubu 70,000

Gwamnoni 20 a Najeriya sun ƙi biyan mafi ƙarancin albashin dubu 70,000

Shugaban ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi ta Najeriya ALGON Alhaji Haruna Ƙanƙara, yace har yanzu akwai jihohi 20 a ƙasar da basu fara biyan sabon tsarin mafi ƙarancin albashi na naira dubu 70 ga ma’aiktan ƙananan hukumomi da malaman makarantun firamare ba.

Shugaban ya ce jihohin sun haɗa da Yobe da Gombe da Zamfara da Kaduna da Imo da Ebonyi da Cross River da Abuja fadar gwamnatin ƙasar da Borno da sauransu.

Shugaban na NULGE ya yi wannan bayani ne a yayin wata zantawa da ya yi da jaridar Punch ta Najeriya, tare da ba da hankali akan biyan mafi ƙarancin albashin a ɓangaren ma’aikatan ƙananan hukumomi da Malaman Makarantun firamare.

Shugaban na Najeriya ya rattaɓa hanu kan ƙudirin dokar biyan naira dubu 70,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi ga ma’aikatan ƙasar ne a ranar 29 ga watan Yulin shekarar 2024, bayan wata yarjejeniya da suka cimma da jagororin ƙungiyar kwadago ta ƙasar.

An kara sabon mafi karancin albashin ne da kashi 133 wato daga N30,000 zuwa N70,000, a daidai lokacin da kasar ke fama da tabarbarewar tattalin arziki.

Da yake bayani kan yadda ake aiwatar da dokar, Kankara ya ce, “A gaskiya muna fuskantar kalubale a jihohi da dama, kamar kimanin 20 da har yanzu basu fara aiwatar da sabon mafi karancin albashi ba.

Ƙanƙara ya ci gaba da cewa ”akwai jihohi kamar Sokoto da Yobe da Gombe da da Zamfara da Kaduna da Imo da Ebonyi da Borno da Cross River da Abuja fadar gwamnatin ƙasar da sauran su, a yayin da wasunsu sun fara biyan sabon tsarin a mataki na jiha sai kuma suka yi watsi da na ƙananan hukumomi da Malaman makarantu, amma muna cigaba da fafutukar ganin an yiwa ma’aikatan adalci”.

Shugaban ya ƙara da cewa “wani ɓangare kuma wasu daga cikin gwamnonin sun alƙawarta cewa zasu biya amma suka gagara biya, sai dai muna iya ƙoƙarin ganin an shawo kan wannan matsalar”

Sannan dangane da batun aiwatar da ‘yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi kuwa, shugaban NULGE ya bayyana cewa har yanzu babban bankin kasar bai tattauna da majalisun ba kan bude asusun ajiyar banki.

“Abin da kungiyar ta ke bukata a koda-yaushe shi ne babban bankin Najeriya ya fitar da wani tsari ga kananan hukumomi da zai basu damar bude asusun ajiya da su, amma har yanzu ba a samu hakan ba”.

Sai dai Shugaban NULGE na jihar Kwara, Seun Oyinlade, ya ce gwamnatin jihar sa ta fara biyan Naira 70,000 ga ma’aikatan jihar tun a watan Oktoban shekarar 2024.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp