Home General Ma’aikatan Nimet sun dakatar da tashin jirgi a jihar Kano

Ma’aikatan Nimet sun dakatar da tashin jirgi a jihar Kano

Zanga-zangar Ma’aikatan hukumar Nimet a filin jirgin saman Malam Aminu Kano dake jihar kano a Arewa maso yammacin Nijeriya ya dakatar da sauka da tashin jiragen sama filin.

Ma’aikatan hukumar sun gudanar da zanga zangar ne bisa abin da suka kira da jan kafa wajen fara biyan su mafi karancin albashi kamar yadda gwamantin tarayyar Nijeriya ta amince da shi.

A wata ganawa da da jaridar Global tracker ta yi da shugaban kungiyar gamayyar kungiyoyin ma’aikatan na  shiyyar arewa maso yammacin Nijeriya Timoty Meshelia, yace baya ga rashin biyan su mafi karancin albashin, akwai kuma hakkokin ma’aikatan na alawus alawus da aka gaza biya.

Kungiyar ta bawa hukumar gudanar filin jirgin saman na Malam Aminu Kano wa’adin wata guda da ta dauki matakan da suka dace wajen magance matsalolin tattalin arziki da ma’aikatan ke fuskanta da suka hadar da biyan su alawus-alawus da kuma samar musu da ingantaccen yanayin aiki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp