Home General Ma’aikatan Nimet sun dakatar da tashin jirgi a jihar Kano

Ma’aikatan Nimet sun dakatar da tashin jirgi a jihar Kano

Zanga-zangar Ma’aikatan hukumar Nimet a filin jirgin saman Malam Aminu Kano dake jihar kano a Arewa maso yammacin Nijeriya ya dakatar da sauka da tashin jiragen sama filin.

Ma’aikatan hukumar sun gudanar da zanga zangar ne bisa abin da suka kira da jan kafa wajen fara biyan su mafi karancin albashi kamar yadda gwamantin tarayyar Nijeriya ta amince da shi.

A wata ganawa da da jaridar Global tracker ta yi da shugaban kungiyar gamayyar kungiyoyin ma’aikatan na  shiyyar arewa maso yammacin Nijeriya Timoty Meshelia, yace baya ga rashin biyan su mafi karancin albashin, akwai kuma hakkokin ma’aikatan na alawus alawus da aka gaza biya.

Kungiyar ta bawa hukumar gudanar filin jirgin saman na Malam Aminu Kano wa’adin wata guda da ta dauki matakan da suka dace wajen magance matsalolin tattalin arziki da ma’aikatan ke fuskanta da suka hadar da biyan su alawus-alawus da kuma samar musu da ingantaccen yanayin aiki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp