Home General Ma’aikatan hukumar NIMET sun janye yajin aiki a Najeriya

Ma’aikatan hukumar NIMET sun janye yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma’aikatan hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NIMET) sun sanar da janye yajin aikin da suka fara kwana biyu da suka gabata bayan wata ganawa da suka yi da ministan sufurin ƙasar.

Yajin aikin da ma’aikatan suka kira, ya haifar da cikas a filayen jiragen sama na cikin gida inda fasinjoji da dama suka kasa yin balaguro.

Ma’aikatan sun yi yajin aikin ne saboda rashin ingantacen yanayin aiki, rashin gudanar da ayyukansu ya kawo cikas a zirga-zirgar jiragen sama a fadin ƙasar ranar Alhamis

Ma’aikatan sun nuna damuwa kan rashin aiwatar da sabon tsarin albashi mafi ƙaƙanta, da batun wasu alawus-alawus, da kuma yin watsi da muhimman shirye-shiryen horas da ma’aikatan da dai sauransu.

Amma bayan wata ganawa da ministan sufurin jiragen saman ƙasar Festus Keyamo a Abuja, ƙungiyar ma’aikatan ta yanke shawarar janye yajin aikin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp