Home General Ma’aikatan hukumar NIMET sun janye yajin aiki a Najeriya

Ma’aikatan hukumar NIMET sun janye yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma’aikatan hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NIMET) sun sanar da janye yajin aikin da suka fara kwana biyu da suka gabata bayan wata ganawa da suka yi da ministan sufurin ƙasar.

Yajin aikin da ma’aikatan suka kira, ya haifar da cikas a filayen jiragen sama na cikin gida inda fasinjoji da dama suka kasa yin balaguro.

Ma’aikatan sun yi yajin aikin ne saboda rashin ingantacen yanayin aiki, rashin gudanar da ayyukansu ya kawo cikas a zirga-zirgar jiragen sama a fadin ƙasar ranar Alhamis

Ma’aikatan sun nuna damuwa kan rashin aiwatar da sabon tsarin albashi mafi ƙaƙanta, da batun wasu alawus-alawus, da kuma yin watsi da muhimman shirye-shiryen horas da ma’aikatan da dai sauransu.

Amma bayan wata ganawa da ministan sufurin jiragen saman ƙasar Festus Keyamo a Abuja, ƙungiyar ma’aikatan ta yanke shawarar janye yajin aikin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp