Home General ‘Yan bindiga sun kashe mutane 28 a wasu sabbin hare-hare a Zamfara

‘Yan bindiga sun kashe mutane 28 a wasu sabbin hare-hare a Zamfara

Aƙalla mutane 28 cikin su har da masu hakar ma’adinai 20 ne ƴan bindiga suka kashe a ranar Alhamis da ta gabata a yayin wasu jerin hare-hare da suka kai ƙaramar hukumar Maru ta jihar Zamfara a arewa maso yammacin Najeriya.

Hare-haren sun auku ne da misalin ƙarfe 11 da rabi na safe akan garuruwan Gobirawa Chali, Damaga da Lugga, hare-haren da mazauna yankunan suka ce sun zo musu a bazata, inda ɗimbin yan bindiga suka kutsa garuruwan nasu a lokaci guda.

Kamfani dillancin labarai na Reuters ya ruwaito wani mazauna garin yana cewa ƴan bindigan sun bude wuta akan masu haƙar ma’adinai, kuma nan ne rikici ya ɓarke har mutane da dama suka mutu.

A wata sanawar da ta fitar a wannan Juma’a, ƙungiyar kare hakkin ɗan adam ta Amnesty ta tabbatar da harin, tana mai cewa maharan sun bi gida-gida a garin Gobirawa Chali, inda suka kashe sama da mutane 20.

A garin Damaga kuwa, mutane biyar ne maharan suka kashe, ayayin da uku suka gamu da ajalinsu a garin Lugga.

Wani mazaunin Lugga ya bayyana yadda ƴan bindigar suka yi ta harbi kan mai uwa da wabi a kewayen ƙauyen, kana suka yi awon gaba da dabbobi.

Rahotanni sun ce dakarun rundunar sojin ƙasar sun kawo ɗauki ba tare da ɓata lokaci ba, abin ma da ya taƙaita ɓarnar kenan.

Dakarun ƙasa da jiragen yaƙin sun shiga garin a yayin harin, inda suka yi bata – kashi, wanda ya kai ga mutuwar ɗimbin maharan.

Waɗannan hare-hare su na nuni da yadda ake cigaba da samun matsalar  tsaro a jihar Zamfara, inda ƴan bindiga suka addabi ƙauyuka da dama, duk kuwa da aikin da sojoji ke yi a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp