Home General ‘Yan bindiga sun kashe mutane 28 a wasu sabbin hare-hare a Zamfara

‘Yan bindiga sun kashe mutane 28 a wasu sabbin hare-hare a Zamfara

Aƙalla mutane 28 cikin su har da masu hakar ma’adinai 20 ne ƴan bindiga suka kashe a ranar Alhamis da ta gabata a yayin wasu jerin hare-hare da suka kai ƙaramar hukumar Maru ta jihar Zamfara a arewa maso yammacin Najeriya.

Hare-haren sun auku ne da misalin ƙarfe 11 da rabi na safe akan garuruwan Gobirawa Chali, Damaga da Lugga, hare-haren da mazauna yankunan suka ce sun zo musu a bazata, inda ɗimbin yan bindiga suka kutsa garuruwan nasu a lokaci guda.

Kamfani dillancin labarai na Reuters ya ruwaito wani mazauna garin yana cewa ƴan bindigan sun bude wuta akan masu haƙar ma’adinai, kuma nan ne rikici ya ɓarke har mutane da dama suka mutu.

A wata sanawar da ta fitar a wannan Juma’a, ƙungiyar kare hakkin ɗan adam ta Amnesty ta tabbatar da harin, tana mai cewa maharan sun bi gida-gida a garin Gobirawa Chali, inda suka kashe sama da mutane 20.

A garin Damaga kuwa, mutane biyar ne maharan suka kashe, ayayin da uku suka gamu da ajalinsu a garin Lugga.

Wani mazaunin Lugga ya bayyana yadda ƴan bindigar suka yi ta harbi kan mai uwa da wabi a kewayen ƙauyen, kana suka yi awon gaba da dabbobi.

Rahotanni sun ce dakarun rundunar sojin ƙasar sun kawo ɗauki ba tare da ɓata lokaci ba, abin ma da ya taƙaita ɓarnar kenan.

Dakarun ƙasa da jiragen yaƙin sun shiga garin a yayin harin, inda suka yi bata – kashi, wanda ya kai ga mutuwar ɗimbin maharan.

Waɗannan hare-hare su na nuni da yadda ake cigaba da samun matsalar  tsaro a jihar Zamfara, inda ƴan bindiga suka addabi ƙauyuka da dama, duk kuwa da aikin da sojoji ke yi a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp