Home General ‘Yan bindiga sun kashe mutane 28 a wasu sabbin hare-hare a Zamfara

‘Yan bindiga sun kashe mutane 28 a wasu sabbin hare-hare a Zamfara

Aƙalla mutane 28 cikin su har da masu hakar ma’adinai 20 ne ƴan bindiga suka kashe a ranar Alhamis da ta gabata a yayin wasu jerin hare-hare da suka kai ƙaramar hukumar Maru ta jihar Zamfara a arewa maso yammacin Najeriya.

Hare-haren sun auku ne da misalin ƙarfe 11 da rabi na safe akan garuruwan Gobirawa Chali, Damaga da Lugga, hare-haren da mazauna yankunan suka ce sun zo musu a bazata, inda ɗimbin yan bindiga suka kutsa garuruwan nasu a lokaci guda.

Kamfani dillancin labarai na Reuters ya ruwaito wani mazauna garin yana cewa ƴan bindigan sun bude wuta akan masu haƙar ma’adinai, kuma nan ne rikici ya ɓarke har mutane da dama suka mutu.

A wata sanawar da ta fitar a wannan Juma’a, ƙungiyar kare hakkin ɗan adam ta Amnesty ta tabbatar da harin, tana mai cewa maharan sun bi gida-gida a garin Gobirawa Chali, inda suka kashe sama da mutane 20.

A garin Damaga kuwa, mutane biyar ne maharan suka kashe, ayayin da uku suka gamu da ajalinsu a garin Lugga.

Wani mazaunin Lugga ya bayyana yadda ƴan bindigar suka yi ta harbi kan mai uwa da wabi a kewayen ƙauyen, kana suka yi awon gaba da dabbobi.

Rahotanni sun ce dakarun rundunar sojin ƙasar sun kawo ɗauki ba tare da ɓata lokaci ba, abin ma da ya taƙaita ɓarnar kenan.

Dakarun ƙasa da jiragen yaƙin sun shiga garin a yayin harin, inda suka yi bata – kashi, wanda ya kai ga mutuwar ɗimbin maharan.

Waɗannan hare-hare su na nuni da yadda ake cigaba da samun matsalar  tsaro a jihar Zamfara, inda ƴan bindiga suka addabi ƙauyuka da dama, duk kuwa da aikin da sojoji ke yi a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp