Home General Ghana ta kora ƴan Najeriya sama da 200 zuwa gida

Ghana ta kora ƴan Najeriya sama da 200 zuwa gida

Gwamnatin Najeriya ta karbi ƴan asalin ƙasar guda 231 da ƙasar Ghana ta koro, 204 daga cikin su fasa ƙwaurinsu akayi zuwa ƙasar.

Bayanai sun ce mutanen sun sauka a filin sauka da tashin jiragen sama na jihar Lagos, ƙarƙashin tarbar hukumar yaƙi da fasa kwaurin ɗan adam ta ƙasar, da kuma hukumar kula da ƴan Najeriya da ke ƙetare da haɗin gwiwar hukumar yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati da shirya laifuffuka ta Ghana.

Da yake Magana yayin karɓar mutanen, shugaban hukumar yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ta‘annati da shirya laifuffuka na Ghana Dominic Mensah yace an kama mutanen ne bayan da jami’an tsaro suka bankaɗo wani tuggun shirin aikata laifi a wani rukunin gidaje guda 50 a ƙasar ta Ghana.

Yace tuni jami’an tsaro suka kama mamallakin gidajen don ci gaba da bincike, yayinda ƴan Najeriyar kuma aka yanke shawarar mayar da su gida.

Cikin mutane 204 da aka dawo da su guda 76 yan asalin jihar Edo ne, sai guda sauran da suka fito daga jihohin Anambra, Delta, Bayelsa, Imo, Enugu, Ebonyi da sauran wasu jihohi.

Wani abu mai tada hankali shine yadda 12 daga cikin mutanen ke zaman ƙananan yara ƴan kasa da shekara 18.

Da take mayar da martani kan wannan batu, shugabar hukumar kula da ƴan Najeriya mazauna ƙetare, Abike Dabiri Erewa ta ce ƴan Najeriya na bukatar wayar da kai na musamman game da illar fasa ƙwaurin ɗan adam da kuma shiga wata ƙasa ba bisa ƙa’ida ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp