Home General Ghana ta kora ƴan Najeriya sama da 200 zuwa gida

Ghana ta kora ƴan Najeriya sama da 200 zuwa gida

Gwamnatin Najeriya ta karbi ƴan asalin ƙasar guda 231 da ƙasar Ghana ta koro, 204 daga cikin su fasa ƙwaurinsu akayi zuwa ƙasar.

Bayanai sun ce mutanen sun sauka a filin sauka da tashin jiragen sama na jihar Lagos, ƙarƙashin tarbar hukumar yaƙi da fasa kwaurin ɗan adam ta ƙasar, da kuma hukumar kula da ƴan Najeriya da ke ƙetare da haɗin gwiwar hukumar yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati da shirya laifuffuka ta Ghana.

Da yake Magana yayin karɓar mutanen, shugaban hukumar yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ta‘annati da shirya laifuffuka na Ghana Dominic Mensah yace an kama mutanen ne bayan da jami’an tsaro suka bankaɗo wani tuggun shirin aikata laifi a wani rukunin gidaje guda 50 a ƙasar ta Ghana.

Yace tuni jami’an tsaro suka kama mamallakin gidajen don ci gaba da bincike, yayinda ƴan Najeriyar kuma aka yanke shawarar mayar da su gida.

Cikin mutane 204 da aka dawo da su guda 76 yan asalin jihar Edo ne, sai guda sauran da suka fito daga jihohin Anambra, Delta, Bayelsa, Imo, Enugu, Ebonyi da sauran wasu jihohi.

Wani abu mai tada hankali shine yadda 12 daga cikin mutanen ke zaman ƙananan yara ƴan kasa da shekara 18.

Da take mayar da martani kan wannan batu, shugabar hukumar kula da ƴan Najeriya mazauna ƙetare, Abike Dabiri Erewa ta ce ƴan Najeriya na bukatar wayar da kai na musamman game da illar fasa ƙwaurin ɗan adam da kuma shiga wata ƙasa ba bisa ƙa’ida ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp