Home General Ghana ta kora ƴan Najeriya sama da 200 zuwa gida

Ghana ta kora ƴan Najeriya sama da 200 zuwa gida

Gwamnatin Najeriya ta karbi ƴan asalin ƙasar guda 231 da ƙasar Ghana ta koro, 204 daga cikin su fasa ƙwaurinsu akayi zuwa ƙasar.

Bayanai sun ce mutanen sun sauka a filin sauka da tashin jiragen sama na jihar Lagos, ƙarƙashin tarbar hukumar yaƙi da fasa kwaurin ɗan adam ta ƙasar, da kuma hukumar kula da ƴan Najeriya da ke ƙetare da haɗin gwiwar hukumar yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati da shirya laifuffuka ta Ghana.

Da yake Magana yayin karɓar mutanen, shugaban hukumar yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ta‘annati da shirya laifuffuka na Ghana Dominic Mensah yace an kama mutanen ne bayan da jami’an tsaro suka bankaɗo wani tuggun shirin aikata laifi a wani rukunin gidaje guda 50 a ƙasar ta Ghana.

Yace tuni jami’an tsaro suka kama mamallakin gidajen don ci gaba da bincike, yayinda ƴan Najeriyar kuma aka yanke shawarar mayar da su gida.

Cikin mutane 204 da aka dawo da su guda 76 yan asalin jihar Edo ne, sai guda sauran da suka fito daga jihohin Anambra, Delta, Bayelsa, Imo, Enugu, Ebonyi da sauran wasu jihohi.

Wani abu mai tada hankali shine yadda 12 daga cikin mutanen ke zaman ƙananan yara ƴan kasa da shekara 18.

Da take mayar da martani kan wannan batu, shugabar hukumar kula da ƴan Najeriya mazauna ƙetare, Abike Dabiri Erewa ta ce ƴan Najeriya na bukatar wayar da kai na musamman game da illar fasa ƙwaurin ɗan adam da kuma shiga wata ƙasa ba bisa ƙa’ida ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp