Home Labarai Barau ya nada shugaban kungiyar zago akida na Kano mukami

Barau ya nada shugaban kungiyar zago akida na Kano mukami

Mataimakin shugaban majalisar dattijan Nijeriya sanata BarauIi. Jibril Maliya ya nada shugaban kungiyar zago akida na jihar Kano Muktar B.A. Gwammaja matsayin maitaimaka masa na musamman.

Wannan na cikin wata takarda da ta fito daga ofishin sanatan mai dauke da sa hannun Mai taimakawa sanatan ta musamman kan harkokin gudanarwa Ngozi Nkemdirim (Mrs) a madadin shugaban ma’aikatan ofishin mataimakin shugaban majalisar wakilan.

Takardar ta ce “Cikin girmamawa ina mai sanarwa da kai cewa an nada ka matsayin mai taimakawa na musamman ga mataimakin shugaban majalisar Dattijan Sanata Barau I. Jibril. Nadin zai fara aiki ne a ranar 1 ga watan Afirilun 2025, har zuwa watan Mayun 2027.”

Kafin nada shi mukamin ya kasance na hannun dama kuma Kuma mataimaki na musamman ga marigayi Amb A.Ahmad Haruna zago akan harkokin yada labarai da aiyuka na musamman, wanda daga bisani ya zama shugaban kungiyar zago akida ta jihar Kano.

Daga bisani sanarwa ta taya Mukhtar Ali (Muktar B.A.A) murna tare da yi masa fatan Alkhairi a nadin da zai taimaki ayyukan sanatan da Nijeriya baki daya.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp