Home General Gwamnatin Tinubu ta firgita da yunƙurin haɗaka – Atiku

Gwamnatin Tinubu ta firgita da yunƙurin haɗaka – Atiku

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta firgita da yunƙurin haɗakar jam’iyyun adawa inda ya ce har yanzu shi ne mafi ƙarfin ɗan adawa a Najeriya.

Ya bayyana hakan ne a matsayin martani ga kalaman Daniel Bwala, tsohon hadiminsa, wanda yanzu haka shi ne mai ba Shugaba Bola Ahmed Tinubu shawara kan harkokin sadarwar manufofi, inda ya shawarci Atiku da ya fasa ƙudirin sake tsayawa takara a 2027.

A wata hira da aka yi da shi a gidan talabiji na Channels, Bwala ya ce Atiku ya kamata ya yarda da ƙaddara, yana mai cewa wataƙila ba nufin Allah bane ya shugabanci Najeriya.

Ya kuma yi ikirarin cewa “Atiku ya rasa kashi 60 zuwa 70 cikin 100 na magoya bayansa, yana mai gargaɗin cewa ci gaba da wannan yunkuri na iya kai shi ga ƙarshe mai raɗaɗi.”

A martanin da ya fito daga ofishin yada labaran Atiku, an siffanta kalaman Bwala da “raini da kuma rashin mutunci,”.

Sanarwar ta ƙara da cewa “ceto da gina Najeriya aikin ne mai matuƙar muhimmanci na ƙasa — wanda bai kamata a bar shi yana tangal-tangal ba saboda son zuciyar wasu hadiman fadar shugaban ƙasa masu neman faranta ran kansu”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp