Home General JAMB ta saka ranar sake jarrabawa a wasu cibiyoyin

JAMB ta saka ranar sake jarrabawa a wasu cibiyoyin

Hukumar shirya jarrabawar shiga manyan makarantu ta Najeriya, Jamb ta amince da saka sabuwar ranar sake jarrabawar UTME ga wasu ɗaliban da suka yi jarrabawar a wasu cibiyoyin rubuta jarrabawar.

A wani taron manema labarai da shugaban hukumar, Farfesa Ishaq Oloyede, ya gabatar a Abuja, babban binrin ƙasar ya ce hukumar ta amince da matsalolin da aka samu a jarrabawar UTME ta 2025,

Ya ƙara da cewa ɗalibai 206.610 ne za su sake jarrabawar a cibiyoyi 65 a Legas, yayin da a Owerri ɗalibai 173,387 za su sake jarrabawar a cibiyoyi 92.

Za a fara sake jarrabawar daga ranar 16 ga watan Mayu, inda za a aike da saƙon waya ga ɗaliban da lamarin ya shafa.

Shugaban hukumar ya kuma nemi afuwar ɗaliban kan matsaloli da aka fuskanta a lokacin jarrabawar.

“Na ɗauki alhakin duk abin da ya faru, kuma ina bayar da haƙuri ga ɗaliban da lamarin ya shafa”, in ji Farfesa Oyodele.

Farfesa Oloyode ya ce matsalar na’ura da aka samu a wasu santocin jihohin Legas da Owerri sun haifar da ƙorafe-ƙorafe daga wasu ɗaliban, inda hukumar ta gano matsalar bayar fitowar sakamakon jarrabawar.

“Matsalar ta samo asali ne daga ɗaya daga cikin kamfanonin da ke bai wa hukumarsu sadarwar, wanda jami’ansa suka kasa magance matsalar ta yadda hakan ya shafi wasu cibiyoyin rubuta jarrabawar,” in ji shugaban hukumar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp