Home General JAMB ta saka ranar sake jarrabawa a wasu cibiyoyin

JAMB ta saka ranar sake jarrabawa a wasu cibiyoyin

Hukumar shirya jarrabawar shiga manyan makarantu ta Najeriya, Jamb ta amince da saka sabuwar ranar sake jarrabawar UTME ga wasu ɗaliban da suka yi jarrabawar a wasu cibiyoyin rubuta jarrabawar.

A wani taron manema labarai da shugaban hukumar, Farfesa Ishaq Oloyede, ya gabatar a Abuja, babban binrin ƙasar ya ce hukumar ta amince da matsalolin da aka samu a jarrabawar UTME ta 2025,

Ya ƙara da cewa ɗalibai 206.610 ne za su sake jarrabawar a cibiyoyi 65 a Legas, yayin da a Owerri ɗalibai 173,387 za su sake jarrabawar a cibiyoyi 92.

Za a fara sake jarrabawar daga ranar 16 ga watan Mayu, inda za a aike da saƙon waya ga ɗaliban da lamarin ya shafa.

Shugaban hukumar ya kuma nemi afuwar ɗaliban kan matsaloli da aka fuskanta a lokacin jarrabawar.

“Na ɗauki alhakin duk abin da ya faru, kuma ina bayar da haƙuri ga ɗaliban da lamarin ya shafa”, in ji Farfesa Oyodele.

Farfesa Oloyode ya ce matsalar na’ura da aka samu a wasu santocin jihohin Legas da Owerri sun haifar da ƙorafe-ƙorafe daga wasu ɗaliban, inda hukumar ta gano matsalar bayar fitowar sakamakon jarrabawar.

“Matsalar ta samo asali ne daga ɗaya daga cikin kamfanonin da ke bai wa hukumarsu sadarwar, wanda jami’ansa suka kasa magance matsalar ta yadda hakan ya shafi wasu cibiyoyin rubuta jarrabawar,” in ji shugaban hukumar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp