Home Labarai Gwamnatin Filato ta zargi jami’an tsaro da rashin kama maharan jihar

Gwamnatin Filato ta zargi jami’an tsaro da rashin kama maharan jihar

Gwamnatin jihar Filato da ke tsakiyar Najeriya ta zargi jami’an sojojin ƙasar da sakaci wajen rashin kama maharan da suka kashe mutum 27 a garin Tahoss na yankin ƙaramar hukumar Riyom.

A farkon makon nan ne wasu mahara ɗauke da makamai suka auka wa garin tare da halaka mutum 27 da raunata wasu.

Yayin wata hira da gidan talbijin na Channels ranar Juma’a ta cikin shirin ”The Morning Brief” kwamishiniyar yaɗa labaran jihar, Joyce Ramnap ta ce sojojin da ke yankin sun nuna sakaci wajen rashin kama ko da mutum guda cikin maharan, duk kuwa da kasancewar sojojin a kusa da garin.

Kwamishiniyar ta ce garin da aka kai harin na kusa da shingen binciken ababen hawa da sojoji ke gudanarwa.

“Akwai shingen binciken ababen hawa na sojoji, wanda bai fi tazarar mita 200 daga wurin da lamarin ya faru, kuma daga bayanan da muka samu ba wanda suka kama, kuma ba su kashe kowa ba”.

“Garin nan ba wani gari ba ne mai nisa da za a ce kafin a kai inda suke an yi musu lahani, suna kusa da titi,” in ji ta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp