Home Labarai Yadda yan bindiga suka yiwa mutane 38 yankan Rago

Yadda yan bindiga suka yiwa mutane 38 yankan Rago

Wasu rahotannin na bayyana cewa Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi musu yankan rago, daga cikin mutum 56 da suka yi garkuwa da su sakamakon gaza biyan kuɗin fansa da ƴanbindigar suke nema.

Mutanen da aka kashe ɗin sun kasance ƴan ƙauyen Banga da ke ƙarƙashin ƙaramar hukumar ƙauran Namoda da ke jihar Zamfara.

kafara BBC ta rawaito yadda Shugaban ƙaramar hukumar, Manniru Haidara Ƙaura wanda ya shaida mata yadda al’amarin ya faru, ya ce yawancin waɗanda aka yi wa yankan ragon matasa ne.

“Bayanin da muka samu shi ne sun yi musu yankan rago ne. Abin da ya faru shi ne ƴanbindigar sun nemi kuɗin fansa kuma aka harhaɗa aka ba su kamar yadda suka nema, inda kuma suka saki mutum 18 da suka haɗa da mata 17 da ƙaramin yaro guda ɗaya, a ranar Asabar,”in ji Haidara.

Kimanin watanni huɗu ne dai ƴan fashin daji suka far wa ƙauyan na Banga da ke ƙaramar hukumar Ƙauran Namoda a jihar ta Zamfara inda suka yi garkuwa da mutum 56.

“Bayanan da suka zo mana shi ne ƴanbindigar sun nemi kuɗin fansa na naira miliyan 50 kuma an ba su amma duk da haka suka zaɓi su kashe mutum 38. Su suka san dalilin kashe su. Mutane ne da ba su da tunani da ba su da hankali. Sun manta ƴanuwansu ne suke kashewa kuma za mu haɗu a gaban Allah.”

Shugaban ƙaramar hukumar ya kuma ƙara da cewa kawo yanzu mutum 16 da suka dawo da su ranar Asabar na asibiti inda ake kula da lafiyarsu, inda gawar su kuma mutum 38 da aka kashe na wurin ƴanbindigar “kamar yadda suka saba ai ba sa bayar da ita.”

Dangane kuma da abin da ya shafi jami’an tsaro a yankin, Manniru Haidara Ƙaura ya ce duk da a wasu wuraren yana jin labarin irin ƙoƙarin da jami’an tsaro ke yi amma a yankinsa labarin ya sha banban.

“Alal haƙiƙanin gaskiya jami’an tsaro ba sa ba mu irin tallafin da ya kamata mu samu daga ɓagarensu ba ma samu….illa dai askarawa na jihar Zamfara su ne kawai suke taimakon mu.”

Jami’an tsaron Najeriya dai musamman sojoji sun sha musanta zarge-zargen da ake yi musu na rashin ka ɗauki a wuraren hare-hare, inda suke cewa jama’a ne ba sa sanar da su da wuri sannan a mafi yawancin lokuta mutane ba su san irin koƙarin da suke yi ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp