Home General Za mu gurfanar da masu karya dokokin hanya a jihar Kano –...

Za mu gurfanar da masu karya dokokin hanya a jihar Kano – KAROTA

Hukumar dake lura da zirga-zirgar ababan hawa a jihar Kano (KAROTA) tayi barazanar gurfanar da dukkan direba ko matukin adaidaita sahu da ya karyar dokokin tuki a kan hanyoyin jihar a gaban kotu domin yi masa hukuncin.

Wannan dai na cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Jami’in yada labaran hukumar Abubakar Ibrahim Sharada ya aikewa PRNigeria, wadda ta ambaci shugaban hukumar Hon. Engr. Faisal Mahmud Kabir na yin gargadin musamman masu ta’adar saba dokokin fitilar mahadar tititunan jihar (Traffic Light) idan an tsayar da su.

wannan na gargadi dai na zuwa ne kwana guda bayan Umarni na Musamman da mai girma gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya bai wa KAROTA, dangane da tabbatar da bin dokokin Fitilun ba da hannu akan hanyoyi da aka sanya a manyan titunan cikin birnin Kano.

Hon. Faisal ya tabbatar da cewa hukumar za ta aiwatar da umarnin Gwamna dari bisa dari, la’akari da cewa gwamnatin Kano na kashe kuɗi masu yawa wajen saka Fitilun ba da hannun da ke amfani da hasken rana domin inganta zirga-zirga a cikin birni.

“Ina so in yaba wa mai girma Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa kulawarsa ga jin daɗin al’ummar Kano, ta hanyar girka waɗannan fitilun Bada hannu akan hanyoyi Masu amfani fa hasken rana da za su rika aiki sa’o’i ashirin da huɗu a kowace rana a kan titunanmu,” inji shi.

Saboda haka, Shugaban ya buƙaci al’ummar jihar, musamman direbobi, da su ba da haɗin kai ga jami’an KAROTA yayin da suke amfani da tituna, domin samun kyakkyawar alaƙa da jama’a.

Ya bayyana cewa, shawarar mai girma Gwamna na dawo da fitilun ba da hannu a manyan tituna da cikin gari na nufin kare rayuka da dukiyoyin jama’a, don haka ya dace kowa ya mutunta wannan tsari ta hanyar bin umarnin ba da hannu da wadan nan Fitulun ke yi akan hanyoyin mu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp