Home General Za mu gurfanar da masu karya dokokin hanya a jihar Kano –...

Za mu gurfanar da masu karya dokokin hanya a jihar Kano – KAROTA

Hukumar dake lura da zirga-zirgar ababan hawa a jihar Kano (KAROTA) tayi barazanar gurfanar da dukkan direba ko matukin adaidaita sahu da ya karyar dokokin tuki a kan hanyoyin jihar a gaban kotu domin yi masa hukuncin.

Wannan dai na cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Jami’in yada labaran hukumar Abubakar Ibrahim Sharada ya aikewa PRNigeria, wadda ta ambaci shugaban hukumar Hon. Engr. Faisal Mahmud Kabir na yin gargadin musamman masu ta’adar saba dokokin fitilar mahadar tititunan jihar (Traffic Light) idan an tsayar da su.

wannan na gargadi dai na zuwa ne kwana guda bayan Umarni na Musamman da mai girma gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya bai wa KAROTA, dangane da tabbatar da bin dokokin Fitilun ba da hannu akan hanyoyi da aka sanya a manyan titunan cikin birnin Kano.

Hon. Faisal ya tabbatar da cewa hukumar za ta aiwatar da umarnin Gwamna dari bisa dari, la’akari da cewa gwamnatin Kano na kashe kuɗi masu yawa wajen saka Fitilun ba da hannun da ke amfani da hasken rana domin inganta zirga-zirga a cikin birni.

“Ina so in yaba wa mai girma Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa kulawarsa ga jin daɗin al’ummar Kano, ta hanyar girka waɗannan fitilun Bada hannu akan hanyoyi Masu amfani fa hasken rana da za su rika aiki sa’o’i ashirin da huɗu a kowace rana a kan titunanmu,” inji shi.

Saboda haka, Shugaban ya buƙaci al’ummar jihar, musamman direbobi, da su ba da haɗin kai ga jami’an KAROTA yayin da suke amfani da tituna, domin samun kyakkyawar alaƙa da jama’a.

Ya bayyana cewa, shawarar mai girma Gwamna na dawo da fitilun ba da hannu a manyan tituna da cikin gari na nufin kare rayuka da dukiyoyin jama’a, don haka ya dace kowa ya mutunta wannan tsari ta hanyar bin umarnin ba da hannu da wadan nan Fitulun ke yi akan hanyoyin mu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp