Home General Gwamnan Kano ya amince da murabus din Kwamishinan Sufuri Ibrahim Ali Namadi

Gwamnan Kano ya amince da murabus din Kwamishinan Sufuri Ibrahim Ali Namadi

Kwamishinan sufurin jihar Kano da ke arewa maso gabashin Najeriya ya ajiye muƙaminsa kan zargin alaƙarsa da mutumin da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi a jihar.

Gwamnatin jihar Kano ce ta sanar da murabus ɗinsa a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar Laraba.

Ibrahim Ali Namadi ya ajiye muƙaminsa na kwamishina ne bayan gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya karɓi rahoton kwamitin binciken zarginsa da hannu a belin Sulaiman Aminu Danwawu, wanda ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi a jihar.

Batun belin Danwawu da ake zargin da hannun kwamishinan, ya ja hankalin jama’ar Kano da ma Najeriya.

“Kwamishinan ya ce ya yanke shawarar yin murabus ne saboda buƙatar al’umma da kuma tasirin al’amarin.”

Sai dai a sanarwar, Kwamishinan ya ci gaba da kare kansa a matsayin marar laifi tare da nisanta kan shi da zargin da ake masa.

“Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da murabus ɗin kwamishinan, tare da yi masa fatan alheri,” kamar yadda Sunusi Bature Dawakin Tofa ya tabbatar

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp