Home General Gwamnan Kano ya amince da murabus din Kwamishinan Sufuri Ibrahim Ali Namadi

Gwamnan Kano ya amince da murabus din Kwamishinan Sufuri Ibrahim Ali Namadi

Kwamishinan sufurin jihar Kano da ke arewa maso gabashin Najeriya ya ajiye muƙaminsa kan zargin alaƙarsa da mutumin da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi a jihar.

Gwamnatin jihar Kano ce ta sanar da murabus ɗinsa a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar Laraba.

Ibrahim Ali Namadi ya ajiye muƙaminsa na kwamishina ne bayan gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya karɓi rahoton kwamitin binciken zarginsa da hannu a belin Sulaiman Aminu Danwawu, wanda ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi a jihar.

Batun belin Danwawu da ake zargin da hannun kwamishinan, ya ja hankalin jama’ar Kano da ma Najeriya.

“Kwamishinan ya ce ya yanke shawarar yin murabus ne saboda buƙatar al’umma da kuma tasirin al’amarin.”

Sai dai a sanarwar, Kwamishinan ya ci gaba da kare kansa a matsayin marar laifi tare da nisanta kan shi da zargin da ake masa.

“Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da murabus ɗin kwamishinan, tare da yi masa fatan alheri,” kamar yadda Sunusi Bature Dawakin Tofa ya tabbatar

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp