Home Labarai Trump ya dakatar da bada biza ga ƴan Najeriya da wasu ƙasashe...

Trump ya dakatar da bada biza ga ƴan Najeriya da wasu ƙasashe 74 ke fara aiki

Donald trump

Yau sabbin dokokin shige da fice na Amurka, wanda Shugaba Donald Trump ya gabatar, na dakatar da aikace-aikacen bada bizar Amurka ga ƙasashe 75, ciki har da na Afirka 26, da suka haɗa da Ivory Coast da Kamaru da Senegal da kuma Najeriya za su fara aiki.

Tun a makon jiya Fadar White House ta sanar da matakin Amurka dakatar da bayar da bizar ƴan ci rani ga ƴan ƙasashe 75, a wani mataki da ta ce yana da nasaba da sake duba tsarin tantance masu neman shiga Amurka.

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta fitar, an umurci dukkan ofisoshin jakadancin Amurka da ke ƙasashe da lamarin ya shafa da su dakatar da bayar da irin waɗannan biza, sanarwar ta bayyana cewa dakatarwar za ta fara aiki ne cikin mako guda, wanda ke daidai wannan Laraba 21 ga watan Janairu, amma ba a fayyace tsawon lokacin da za a ɗauka kafin a janye ta ba.

Dakatarwar ta shafi biza iri-iri, na bakin haure da waɗanda ba bakin haure ba, tsabanin bizar yawon shaƙatawa, wannan mataki ya mayar da hankali kan tafiya Amurka don neman aiki ko karatu ko haɗuwar iyali.

Ba’a bayyana sunayen ƙasashen 75 da wannan sabon mataki ya shafa ba, amma majiyoyi sun ce dakatarwar ta shafi Rasha da Iran da Afghanistan da Thailand da Brazil da wasu ƙasashen Afirka, ciki harda Najeriya.

Ga shugaba Donald Trump, gwamnati da ɗauki wannan mataki ne domin aiwatar da sauye-sauye a fannin shige da fice, domin tabbatar da cewa baƙi sun kasance masu dogaro da kansu a fannin kuɗi, amma ba masu zama jidali ga Amurkawa ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp