Home Labarai Trump ya dakatar da bada biza ga ƴan Najeriya da wasu ƙasashe...

Trump ya dakatar da bada biza ga ƴan Najeriya da wasu ƙasashe 74 ke fara aiki

Donald trump

Yau sabbin dokokin shige da fice na Amurka, wanda Shugaba Donald Trump ya gabatar, na dakatar da aikace-aikacen bada bizar Amurka ga ƙasashe 75, ciki har da na Afirka 26, da suka haɗa da Ivory Coast da Kamaru da Senegal da kuma Najeriya za su fara aiki.

Tun a makon jiya Fadar White House ta sanar da matakin Amurka dakatar da bayar da bizar ƴan ci rani ga ƴan ƙasashe 75, a wani mataki da ta ce yana da nasaba da sake duba tsarin tantance masu neman shiga Amurka.

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta fitar, an umurci dukkan ofisoshin jakadancin Amurka da ke ƙasashe da lamarin ya shafa da su dakatar da bayar da irin waɗannan biza, sanarwar ta bayyana cewa dakatarwar za ta fara aiki ne cikin mako guda, wanda ke daidai wannan Laraba 21 ga watan Janairu, amma ba a fayyace tsawon lokacin da za a ɗauka kafin a janye ta ba.

Dakatarwar ta shafi biza iri-iri, na bakin haure da waɗanda ba bakin haure ba, tsabanin bizar yawon shaƙatawa, wannan mataki ya mayar da hankali kan tafiya Amurka don neman aiki ko karatu ko haɗuwar iyali.

Ba’a bayyana sunayen ƙasashen 75 da wannan sabon mataki ya shafa ba, amma majiyoyi sun ce dakatarwar ta shafi Rasha da Iran da Afghanistan da Thailand da Brazil da wasu ƙasashen Afirka, ciki harda Najeriya.

Ga shugaba Donald Trump, gwamnati da ɗauki wannan mataki ne domin aiwatar da sauye-sauye a fannin shige da fice, domin tabbatar da cewa baƙi sun kasance masu dogaro da kansu a fannin kuɗi, amma ba masu zama jidali ga Amurkawa ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp