Home Labarai Trump ya dakatar da bada biza ga ƴan Najeriya da wasu ƙasashe...

Trump ya dakatar da bada biza ga ƴan Najeriya da wasu ƙasashe 74 ke fara aiki

Donald trump

Yau sabbin dokokin shige da fice na Amurka, wanda Shugaba Donald Trump ya gabatar, na dakatar da aikace-aikacen bada bizar Amurka ga ƙasashe 75, ciki har da na Afirka 26, da suka haɗa da Ivory Coast da Kamaru da Senegal da kuma Najeriya za su fara aiki.

Tun a makon jiya Fadar White House ta sanar da matakin Amurka dakatar da bayar da bizar ƴan ci rani ga ƴan ƙasashe 75, a wani mataki da ta ce yana da nasaba da sake duba tsarin tantance masu neman shiga Amurka.

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta fitar, an umurci dukkan ofisoshin jakadancin Amurka da ke ƙasashe da lamarin ya shafa da su dakatar da bayar da irin waɗannan biza, sanarwar ta bayyana cewa dakatarwar za ta fara aiki ne cikin mako guda, wanda ke daidai wannan Laraba 21 ga watan Janairu, amma ba a fayyace tsawon lokacin da za a ɗauka kafin a janye ta ba.

Dakatarwar ta shafi biza iri-iri, na bakin haure da waɗanda ba bakin haure ba, tsabanin bizar yawon shaƙatawa, wannan mataki ya mayar da hankali kan tafiya Amurka don neman aiki ko karatu ko haɗuwar iyali.

Ba’a bayyana sunayen ƙasashen 75 da wannan sabon mataki ya shafa ba, amma majiyoyi sun ce dakatarwar ta shafi Rasha da Iran da Afghanistan da Thailand da Brazil da wasu ƙasashen Afirka, ciki harda Najeriya.

Ga shugaba Donald Trump, gwamnati da ɗauki wannan mataki ne domin aiwatar da sauye-sauye a fannin shige da fice, domin tabbatar da cewa baƙi sun kasance masu dogaro da kansu a fannin kuɗi, amma ba masu zama jidali ga Amurkawa ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp