Home Labarai Trump ya dakatar da bada biza ga ƴan Najeriya da wasu ƙasashe...

Trump ya dakatar da bada biza ga ƴan Najeriya da wasu ƙasashe 74 ke fara aiki

Donald trump

Yau sabbin dokokin shige da fice na Amurka, wanda Shugaba Donald Trump ya gabatar, na dakatar da aikace-aikacen bada bizar Amurka ga ƙasashe 75, ciki har da na Afirka 26, da suka haɗa da Ivory Coast da Kamaru da Senegal da kuma Najeriya za su fara aiki.

Tun a makon jiya Fadar White House ta sanar da matakin Amurka dakatar da bayar da bizar ƴan ci rani ga ƴan ƙasashe 75, a wani mataki da ta ce yana da nasaba da sake duba tsarin tantance masu neman shiga Amurka.

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta fitar, an umurci dukkan ofisoshin jakadancin Amurka da ke ƙasashe da lamarin ya shafa da su dakatar da bayar da irin waɗannan biza, sanarwar ta bayyana cewa dakatarwar za ta fara aiki ne cikin mako guda, wanda ke daidai wannan Laraba 21 ga watan Janairu, amma ba a fayyace tsawon lokacin da za a ɗauka kafin a janye ta ba.

Dakatarwar ta shafi biza iri-iri, na bakin haure da waɗanda ba bakin haure ba, tsabanin bizar yawon shaƙatawa, wannan mataki ya mayar da hankali kan tafiya Amurka don neman aiki ko karatu ko haɗuwar iyali.

Ba’a bayyana sunayen ƙasashen 75 da wannan sabon mataki ya shafa ba, amma majiyoyi sun ce dakatarwar ta shafi Rasha da Iran da Afghanistan da Thailand da Brazil da wasu ƙasashen Afirka, ciki harda Najeriya.

Ga shugaba Donald Trump, gwamnati da ɗauki wannan mataki ne domin aiwatar da sauye-sauye a fannin shige da fice, domin tabbatar da cewa baƙi sun kasance masu dogaro da kansu a fannin kuɗi, amma ba masu zama jidali ga Amurkawa ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp