Home SIYASA Rikicin Rasha da Ukraine: Kada Wanda ya ci ko Sha Wani Abu...

Rikicin Rasha da Ukraine: Kada Wanda ya ci ko Sha Wani Abu a Wajen Taron Neman Zaman Lafiya – Ministan Ukraine

Rikicin Rasha da Ukraine: Kada Wanda ya ci ko Sha Wani Abu a Wajen Taron Neman Zaman Lafiya – Ministan Ukraine

 

Ministan harkokin wajen Ukraine, Dmytro Kuleba, ya bai wa mahalarta taron tattaunawar da ake yi da Rasha shawara cewa kada wanda ya ci ko ya sha wani abu a wajen.

Ministan ya ba da shawarar ce gabanin fara taron da za a yi a Turkiyya.

Kafar yada labaran Ukraine ce ta bayyana hakan inda ta ce ministan ya bada shawararce bayan zargin da aka yi cewa an bai wa shahararren attajirin nan Roman Abramovich guba a farkon tattaunawar zaman lafiyar da aka yi a farkon watan nan.

Akwai shakku a kan zargin da ake a kan zargin bai wa Mr Abramovich guba, inda wani jami’a a Amurka da ba a bayyana sunansa ba ya shaida wa kamfanin dillancin na Reuters cewa ba mamaki canjin yanayi ne ya shafi Mr Abramovich.

A ci gaba da tattaunawar ta yau a kan rikicin Rasha da Ukraine, Abramovich ya isa wajen a cewar kafar yadda labaran Turkiyya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp