Rikicin Rasha da Ukraine: Kada Wanda ya ci ko Sha Wani Abu a Wajen Taron Neman Zaman Lafiya – Ministan Ukraine

Rikicin Rasha da Ukraine: Kada Wanda ya ci ko Sha Wani Abu a Wajen Taron Neman Zaman Lafiya – Ministan Ukraine

 

Ministan harkokin wajen Ukraine, Dmytro Kuleba, ya bai wa mahalarta taron tattaunawar da ake yi da Rasha shawara cewa kada wanda ya ci ko ya sha wani abu a wajen.

Ministan ya ba da shawarar ce gabanin fara taron da za a yi a Turkiyya.

Kafar yada labaran Ukraine ce ta bayyana hakan inda ta ce ministan ya bada shawararce bayan zargin da aka yi cewa an bai wa shahararren attajirin nan Roman Abramovich guba a farkon tattaunawar zaman lafiyar da aka yi a farkon watan nan.

Akwai shakku a kan zargin da ake a kan zargin bai wa Mr Abramovich guba, inda wani jami’a a Amurka da ba a bayyana sunansa ba ya shaida wa kamfanin dillancin na Reuters cewa ba mamaki canjin yanayi ne ya shafi Mr Abramovich.

A ci gaba da tattaunawar ta yau a kan rikicin Rasha da Ukraine, Abramovich ya isa wajen a cewar kafar yadda labaran Turkiyya.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 26 minutes 30 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 7 minutes 55 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here