• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home SIYASA Sayen form din takarar gwamna da injinya Magaji Mu’azu yayi yaja cece-kuce
  • SIYASA

Sayen form din takarar gwamna da injinya Magaji Mu’azu yayi yaja cece-kuce

By
Prnigeria
-
April 9, 2022
Arewa Award

Sayen form din takarar gwamna da injinya Magaji Mu’azu yayi yaja cece-kuce

Read Also:

  • Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin Mota
  • NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta
  • Kotun Ƙolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kisa kan Maryam Sanda

Sayen form din takarar gwamna da injinya Magaji Mu’azu yayi yaja cece-kuce
Tsohon kwamishinan ayyuka na jihar Kano ya sayi fam din tsayawa takarar Gwamnan jihar karkashin Inuwar Babbar Jam’iyya adawa ta PDP.
Ya shaidawa Politics Digest cewa zai rika bayyanawa magoya bayan sa muhimman kudirce kudircen daya yake dasu, da kuma fannin da zai mayar da hankali kacokan a yayin da yake fafutukar daukar wannan muhimmin nauyin.
“Wannan tafiya nasara ce ga Al’umma Kano da kuma Arewacin Nijeriya da kasa baki daya.
“Zahiri mun dauki gabarar tafiyar Kano Sabuwa, bayan mun roki tai makon Allah, muna bukatar Addu’oin Al’umma da goyan bayan su” in ji Mu’azu.
Mu’azu Ahmad Magaji, wanda aka fi sani da (Dansarauniya) injiniyan Man Fetur da Iskar Gas dan fafutuka kuma guda cikin ‘yan siyasa a Nijeriya dan asalin Jihar Kano.
An haifeshi a kauyen sarauniya dake Karamar Hukumar Dawakin Tofa ta jihar Kano.
ya sami shaidar kammala Makarantar Firamare a shekarar 1980; ya kuma halarci Makarantar Sakandire ta Dawakin Tofa a tsakanin 1980 zuwa 1980, ya yi karatun Diploma a fannin Injiniya a kwalejin kere-kere ta jihar Kano (Polytechnic) a shekarar 1989. Ya kuma sami Digrin sa na farko a wannin fanni na Injiniya a Jami’ar Bayero dake jihar Kano, inda ya sami Digrin Sa na biyu a jami’ar Robert Gordon a shekarar 2000. Ya kuma sami cancanta a fannin sarrafa ayyukan, Injiniyan Rijiyar Man Fetur da Iskar Gas, Kimiyyar kasa da Bayanai a shekara 2006.
Mu’azu ya fara aiki a Hukumar Da’ar Ma’aikata ta Jihar Kano a shekarar 1989 ku ya yi ritaya a shekarar 2009, in da ya fara aiki da kamfanin Mai na shell har na tsawon shekaru 10
A shekara 2010 Shugaban Kasa Godluck Jonathan ya nada shi matsayin ko’odinata na Shirin gwamnatin tarayya na Sure-P inda yayi aiki daga shekarar 2010 zuwa shekarar 2013.
Ya kuma yi aiki tare da gwamnan Jihar Kano Engr. Dr. Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin Babban Mataimaki na Musamman Kan Tsare-Tsare tsakanin shekarar 2013 zuwa 2015. Ya kuma tsaya takarar Kujerar Gwamnan Jihar Kano a shekarar 2014 ya kuma janye kafin gudanar da zaben cikin gida (Primary Election).
An kuma nada Mu’azu matsayin Kwamishinan Ayyuka a karkashin Gwamnan Jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje a shekarar 2019, in da aka cire shi daga mukamin a shekarar 2020 lokacin da yayi wani kalamai da akayi zargin na rashin da’a ne game da mutuwa Shugaban Ma’aikatan fadar Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, Abba Kyari, wanda ya mutu sakamakon kamuwa da cutar Corona (COVID-19).
Daga bisani Mu’azu ya kamu da cutar ta corona bayan gwajin da aka gudanar a kan sa inda aka killace shi, daga bisani kuma aka sallame shi bayan an gudanar da gwajin daya nuna ya warke daga cutar ta corona.
Sai dai Gwamnan jihar kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sake nada shi a Mukamin Shugaban Kwamitin Sanya Idanu kan yadda Aikin Shimfida Bututun Iskar Gas na NNPC-AKK da kuma habaka Masana’antun Jihar Kano.
By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • Magaji Muazu
Previous articleHarin Dakarun Rundunar Sojin Najeriya Ya Hallaka Kwamandan da Mayakan ISWAP a Marte Dake Jihar Borno
Next articleRundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta Kame ‘Yan Kungiyar Asiri Guda 32 a Jihar Anambra
Prnigeria

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Babu sauran sakaci a jam’iyyarmu ta PDP – Kabiru Turaki

Tinubu ya taya Kwankwaso munar cika shekaru 69 a duniya

Ban koma jam’iyyar APC ba – Namadi Sambo

Barau ya nada shugaban kungiyar zago akida na Kano mukami

Nima ɗan ƙungiyar Zago Akida ne -Sanata Barau

Gwamnoni ku dauki aniyar hidimtawa Al’umma – buhari

Atiku ya yi martani kan kalaman Akume ga ‘yan Arewa

An sake zaɓar Okonjo-Iweala shugabar WTO a wa’adi na biyu

Dalilin Ndume na sa alamar tambaya kan gaggawar amincewa da ƙudurin haraji na Tinubu

Yahaya Bello ya musanta zargin rashawa a gaban kotu

Hukumar EFCC ta ce ta yi nasarar kama Yahaya Bello

PDP ta yi watsi da sakamakon zaɓen jihar Ondo

Recent Posts

  • Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin Mota
  • NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta
  • Kotun Ƙolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kisa kan Maryam Sanda
  • Kotu ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige gidan yari
  • Har yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso – Tugga

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1642 days 4 hours 33 minutes 47 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1624 days 6 hours 15 minutes 12 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin MotaNNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar DeltaKotun Ƙolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kisa kan Maryam SandaKotu ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige gidan yariHar yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso - TuggaNajeriya ta ce jirgin ta ya yi saukar gaggawa ne a Burkina FasoBurkina Faso ta tsare jirgin sojin Najeriya kan keta sararin samaniyar ƙasarKwankwaso ya ce matsalar tsaro na neman fin karfin Gwamnatin NijeriyaAn ceto wasu daga cikin daliban da aka sace a makarantar Papiri da ke jihar NejaAmnesty ba bukaci a gaggauta sakin Muhuyi MagajiAkwai sa hannun 'yan siyasa a kamen da aka yiwa Muhuyi - Gwamnatin KanoMajalisa ta amince da naɗin Chris Musa ministan tsaron NajeriyaWadanda aka sace a Cocin jihar Kwara sun shaki iskar 'yanciGwamnatin Nasarawa za ta kafa ƴan sandan JihaGwamnan Osun Ademola Adeleke ya fice daga jam’iyyar PDP
X whatsapp