Home SIYASA An Fara Kace Nace Tsakanin Tinubu da Osibanjo

An Fara Kace Nace Tsakanin Tinubu da Osibanjo

Jagoran jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya, kuma Dan Takarar Shugabancin Qasa karkashin Inuwar Jam’iyyar, Bola Ahmad Tinubu yace Mataimakin Shugaban Kasa Farfesa Yemi Osibanjo ba Dan sa bane.

Ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai a yammacin ranar Litinin a Birnin Tarayya Abuja, jim kadan bayan kammala ganawar sa da Gwamnonin Jam’iyyar APC su 12.

Ganawar da aka yi a masaukin Gwamnan Jihar Kebbi, a Asokoro dake Birnin tarayya Abuja, ta zo bayan Mataimakin Shugaban Kasa Yemi Osibanjo ya bayyana Kudirin sa na tsayawa takarar Shugaban Kasa a kakar zaben shekarar 2023.

Da aka tambaye shi don yin tsokaci dangane da Takarar Mataimakin Shugaban Kasar, wanda ake masa kallon dansa ne a siyasance, Tinubu yace “Bani da wani da da ya girma da zai iya yin Takarar shugaban kasa, “Bani da wani Da daya girma zai iya wannan furuci.

Sai dai yace ya ganawa da gwamnonin jihohin ne domin neman hadin kai, goyon baya da karfafa Gwuiwa dangane da burin sa na tsayawa takarar shugabancin Nijeriya a shekarar 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp