Home Labarai ‘Yan Sanda a Jihar Zamfara Sun Sami Nasarar Kubutar da Mutane 39...

‘Yan Sanda a Jihar Zamfara Sun Sami Nasarar Kubutar da Mutane 39 da Hannun ‘Yan Bindiga

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya ta sami nasarar kubutar da mutum 39 Mafi yawan su mata da kananan Yara da ‘Yan Bindiga sukayi garkuwa dasu a  jihar Zamfara.

Kakakin hukumar ‘Yan Sandan Jihar ta Zamfara Muhammad Shehu, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa, inda yace wadanda aka kubutar din na cikin wadanda ‘Yan bindigar sukayi garkuwa dasu a kauyukan dake kananan hukumomin Maru da Bungudu.

“Wadanda aka kubutar sun hadarda Maza 8 Mata 15 cikin su harda masu shayarwa da kuma kananan yara 16” a cewar sa.

“Nasarar ta biyo bayan wani aikin share fage da Rundunar ‘Yan Sanda hadin Gwuiwa da Rundunar Soji suka gudanar a sansanin Dabar Magaji dake dajin Kadanya wanda ke tsakanin Kananan Hukumomin Kaura Namoda da Maradun.

Ya kara da cewa, “ ‘Yan sanda da hadin gwuiwar kungiyar likitocin Gwamnatin Jihar sun dukufa domin bawa wadanda aka ceto kulawa ta musamman, inda daga bisani kuma za’a mika su ga iyalan su, a cewar sa.

Rundunar ‘Yan Sandan ta ce ta sami nasarar kame wasu mutum 10 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban daga cikin su akwai ‘yan haramtacciyar kungiyar ‘yan Sakai.

Yan Sakai kungiya ce ta ‘Yan banga da ke aiki a cikin yankin Arewa Maso Yamma, yawancin su mafarauta ne da ke aiki da Jami’an tsaro don kare Al’ummarsu daga ‘Yan fashin da ke kai farmaki a kauyuka da gonaki.

Daga cikin mutane goman da rundunar ta sami nasarar kamawa akwai mutum 3 da ake zargi da yin garkuwa da mutane 2 a unguwar fakon Idi dake talata mafarada kuma wasu mutane 2 da aka kama da laifin shiga gidaje da satar wayoyin hannu a Gusau babban birnin jihar ta Zamfara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp