Home Labarai TSARO: Dakarun MNJTF Sun Sake Halaka Kwamandan Mayakan ISWAP da Mayakan Kungiyar...

TSARO: Dakarun MNJTF Sun Sake Halaka Kwamandan Mayakan ISWAP da Mayakan Kungiyar 15

Dakarun Rundunar Sojin Hadin Gwuiwa MNJTF sun sami nasarar halaka mayakan kungiyar tada kayar baya ta Boko Haram tsagin ISWAP, Abu Fatima da wasu Karin Mayakan Kungiyar 15, a wani gagarunmin hari da suka kai maboyar mayakan a yankin Tafkin Chadi.

A ranar 9 ga Afrilun, 2022 jirgin yaki samfurin Super Tucano bisa sarrafawar Rundunar Sojin Sama karkashin Dakarun na MNJTF da kuma dakarun Mi35 hadi da dakarun Mi171 sukayi barin wuta kan dabar mayakan na ISWAP dake a arewacin Jubularam a Karamar Hukumar Marte dake jihar Borno.

Wani jami’in liken asiri ya shaidawa PRNigeria cewa an kai harin ne ta sama bayan wasu bayanan sirri da aka samu kan cewa kwamandan na ISWAP na Shirin yin fito na fito da Dakarun Sojin, nan rundunar sojin  ta dauki matakin kai harin.

Kwamandan Mayakan na ISWAP Abu-Fatima na da mayaka 500 a karkashin sa, kuma shike lura da yankunan Kirta Wulgo, Sabon Tumbu, Kwaleram, Sigir da Jibularam, Abbaganaram da Yarwa Kura.

Majiyar ta shaida cewa kwamandan ya jagoranci mabanbanta hare haren da aka kaiwa dakarun sojin Najeriya a garuwan da dama ciki har da Kukawa, Abadam, Malam Fatori duk a karamar hukumar Marte.

Zafafa hare-haren da dakarun sojin ke yi ta sama wanda COIN ke jagoranta, ya sanya mayakan na Boko Haram tsagin ISWAP neman mafaka a yankin riversbanks dake tsakanin Nijeria da jamhuriyar Niger.

Sabbin mabuyar ‘Yan kungiyar ta ISWAP sun hadar da Lumburam, Fiyoo, Lada da Jarwaram, dukkan su a yankin na riverbanks.

Wata majiya ta shaidawa PRNigeria cewa a ranar 11 ga Afrilu an shigo da wasu makamai da suka hadar manyan bindigun Atilare cikin garin Tudun Wulgo da mashigar Bakkassi dake kasar Kamaru.

A yayin wata huduba salar juma da guda cikin kwamandojin kungiyar ta ISWAP ya gabatar a Sabon Tumbu, bukaci mayakan kungiyar su sake jajircewa wajen kare Daular daga farmakin soji.

Dakarun sojin hadin gwuiwar karkashin Operation lake and Desert sanity, na cigaba da kai hare-hare kan maboyar ‘yan ta’addar da suka hadar da cikin surkukin daji kan Tsaunuka, ruwa da dukkan maboyan ‘yan ta’addar da suka addabi yankin Arewa maso gabashin Nijeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp