Home Labarai Gwamnatin Jihar Niger ta Tabbatar da Halaka ‘Yan Bindiga a Garin Shiroro

Gwamnatin Jihar Niger ta Tabbatar da Halaka ‘Yan Bindiga a Garin Shiroro

 

Wani rahoto ya bayyana cewa, hankalin Gwamnatin jihar Niger ya kai kan wani labari da ake yadawa a kafar sada zumunta ta zamani da sauran kafafen sadarwa, cewa wani harin Jami’an tsaro ta sama yayi sanadiyyar mutuwar wasu fararen hula a garin Kurebe dake Karamar Hukumar Shiroro a Jihar.

Wannan na cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Kwamishinan Kananan Hukumomi da masarautu na jihar Emmanuel Umar, wadda aka aikewa PRNigeria.

Sanarwar tace Gwamnatin jihar ta bayyana cewa a iyaka sanin ta babu wani farar hula daya rasa ransa sakamakon harin, haka kuma babu wani mazaunin garin da aka tilastawa shiga ko zuwa neman abinda zai ci a sansanin ‘ya gudun hijira a jihohi makotan jihar.

Gwamnatin Jihar ta Niger ta yi maraba da matakin kakkabe ‘Yan ta’adda da Rundunar Sojin Nijeriya ta dauka a  jihohin dake makotaka da jihar, da wasu kananan hukumomin jihar ciki harda kananan hukumomin Shiroro, Munya da sauran sun, matakin da yayi sanadiyyar kawar da ‘yan ta’adda masu tarin yawa a yankin.

Sanarwar tace gwamnatin jihar tayi matukar farin ciki da wannan  atisayen sakamakon nasarar da yake samu na halaka ‘yan bindiga a kananan hukumomin da lamarin ya shafa, wannan hadakar ta taimaka matuka wajen dakile ayyukan ‘yan ta’addan a kanana hukumomin Munya da Shiroro, tare da kubutar da wasu mutane da dama.

Daga bisani Gwamnatin Jihar ta nuna jindadin bisa nasarar da dakarun hadin Gwuiwar ke samu, tare da karin karfin gwuiwar cigaba da kakkabe su daga cikin Al’ummar dake yankin, domin su sami damar komawa gonakin su da cigaba da ayyukan su na yau da kullum.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp