Home Labarai ISWAP Ta Hallaka Tsohon Mashawarci Ga Abubakar Shekau

ISWAP Ta Hallaka Tsohon Mashawarci Ga Abubakar Shekau

Kungiyar ta da kayar baya ta Boko Haram tsagin ISWAP, sun hallaka tsohon mataimaki na musamman ga Abubakar Shekau, bayan yayi kokarin mika wuya.

Jaridar PRNigeria ta rawaito cewa mayakan na ISWAP sun halaka Abu-sadiq Burbur, bisa zargin sa da shirin mika wuya ga Dakarun Rundunar Sojin Nijeriya.

Wata Majiya mai tushe ta shaidawa PRNigeria cewa an halaka Burbur ne a kauyen Galta da ke kusa da Madagali bayan kungiyar ISWAP ta tuhume shi da laifin cin amanar kasa.

inda daga bisani aka gurfanar da shi a wata kotun masu tada kayar dake zaman ta a dajin Sambisa wadda Ya-shaik guda cikin mayakan na ISWAP ke jagoranta.

Burbur dai tsohon mashawarci ne ga tsohon shugaban kungiyar Boko Haram Abubakar shekau.

Ana dai kallon wannan lamari na mika wuya da mayakan na kungiyoyin tada kayar bayan ke yi a ‘yan tsakanin nan nada nasaba da ruwan wuta gami da farmaki da dakarun sojin ke kai musu babu kakkautawa a maboyar su

 

By PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp