Home Labarai Babban Mai Tace Labarai Na Jaridar PRNigeria Ya Rasa Mahaifin Sa.

Babban Mai Tace Labarai Na Jaridar PRNigeria Ya Rasa Mahaifin Sa.

Babban mai tace labarai na jaridar PRNigeria, Yusha’u Shuib ya rasa mahaifin sa Shiek Abdulhameed Agaka mai kimanin shekaru 77 a duniya.

Sheik Abdulhameed, sananne addinin islama ne kuma babban limamin garin Agaka dake karamar hukumar Ilorin da yamma dake jihar kwara, ya koma ga mahaccinsa sakamakon wata gajiriyar rashin lafiya a ranar asabar.

Tunu aka gudanar da jana’idar sa kamar yadda addinin musulunci ya tanadar a ranar lahadi a gidan sa dake garin na Agaka.

An haifi malamin a zuri’ar Imam Shuaib Said, mashahurin malamin addini, kuma masanin Al’kurani mai tsarki jagoran addinin muslunci a garin na Agaka.

Babban limamn na Agaka yayi karatun sa a makarantar School for Arabic Studies wato (SAS) dake jihar Kano daga bisani ya tafi Jami’ar Bayero dake jihar ta kano inda ya sami babban Digiri a fannin ilimin Alqur’ani a da kuma Nahawun Harshen Larabci.

Shaihin malamin a lokuta da daban-daban ya kasance shugaban sashen Nazarin harshen larabci a kwalejin ilimin addinin Musulunci da shari’a ta kano wato Aminu kano College of legal and Islamic studies.

Fatan Allah ya gafarta masa ya kuma inganata abinda ya bari yasa Aljanna ce makomar sa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp