Home Labarai ‘Yan Sanda Sun Halaka ‘Yan Ta’adda Tare Da Kama Wadda Ke Musu...

‘Yan Sanda Sun Halaka ‘Yan Ta’adda Tare Da Kama Wadda Ke Musu Safarar Makamai A Kaduna

Dakarun rundunar yan sandan Nijeriya ta musamman dake birnin tarayya Abuja hadin gwuiwa da Dakarun Operation Yaki sun sami nasarar halaka ‘yan Ta’adda guda 4 tare da kame wata mata dake musu safarar Alburusai akan babbar hanyar Saminaka zuwa Jos a Jihar Kaduna.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar DSP Mohammed Jalige ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da aka rana ga manema labarai, sanarwar tace lamarin ya auku ne ranar laraba 15 ga watan Yuni, yayi da ‘yan sandan suka kama ‘yan bindigar cikin wata shudiyar mota (blue) wadda James Dawi mai kimanin shekaru 31 dan asalin garin Vom na karamar hukumar Jos ta kudu a Jihar Plateau.

Sanarwa ta kara da cewa maharani sun gamu da gamon su a hanayar su ta kai wasu muggana makamai ga tawagarsu, inda suka yi musayar wuta da jami’an.

“kwararrun Jami’an sun sami nasarar raunata wasu mutane 4 da ake zargi. Yayin da aka garzaya da su asibitin koyarawa na Barau Dikko dake Kaduna, inda likitoci suka tabbatar da mutuwar su, said ai ya tabbatar da cewa wasu cikin ‘yan bindiga sun tsere daji da raunukan harbi a cikin su.

Ya kara da cewa yayin da dakarun ke gudanar da bincike a cikin motar, an gano bindiga kirar AK49 guda 1dauke da alburusai guda 6, tare da wani kwanson masakin alburushin, da kuma wasu tarin Alburusai guda 134 da kuma wata mota guda 1.

Yace dakarun a yayin atisayen sun kuma kama wata mata, wadda da ake gudanar da bincike ta amsa cewa ita ke yiwa ‘yan bindigar safarar makamai a jihar Kaduna.

Daga bisani ya bayyana cewa hanzu haka dai hukumar ‘yansandan jihar na zurfafa bincike kan lamarin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp