Home Labarai A karkashin Mulkin Buhari, An Hallaka Sama Da Mutum 3,478, An Sace...

A karkashin Mulkin Buhari, An Hallaka Sama Da Mutum 3,478, An Sace 2,256

Wani rahoton bincike a Najeriya ya ce akalla mutane dubu 3 da 478 aka kashe a Najeriya tsakanin watan Disambar bara zuwa Yunin bana, yayin da aka sace wasu dubu 2 da 256 sakamakon tabarbarewar tsaron da ya addabi kasar.

Kungiyar da ke sanya ido akan harkokin tsaro da ake kira ’Nigeria Security Tracker’ da ke samun goyan bayan wata Majalisa a Amurka ta gabatar da wadannan alkaluma masu tada hankali.

Rahotan kungiyar ya danganta kisan da kuma sace mutanen da akayi a cikin watanni 7 da suka gabata da ayyukan ‘Yan ta’adda da ‘Yan bindiga da ‘Yan fashi da makami da ‘Yan kungiyar asiri da kuma jami’an tsaro.

Alkaluman da kungiyar ta gabatar yace a watan Disambar bara, an kashe ‘Yan Najeriya 342, yayin da aka sace wasu 397, cikin wadanda aka kashe harda manoma 45 a Jihar Nasarawa da kuma mata 34 da aka sace a Jihar Zamfara.

A watan Janairun wannan shekara, kungiyar tace akalla mutane 844 aka kashe, yayin da aka sace 603, cikin su harda mutane sama da 200 a yankunan Jihar Zamfara da 220 da aka kasha a Neja, sai kuma 200 da aka sace a Jihar.

A watan Fabarairu kuma, kungiyar tace mutane 495, bayan sace 326, cikin su harda 33 wadanda suka ki biyan harajin naira miliyan 40 da yan bindiga suka sanya musu a Jihar Zamfara, sai kuma 44 da aka kashe a Jihar Neja, tare da sace 31.

Sakamakon binciken yace a watan Maris, mutane 606 akayi asarar rayukan su, tare da sace wasu 450 cikin su harda Yan Sakai 63 a Jihar Kebbi da kuma mutane 26 da aka kashe a harin da ake danganta shi da ramako a Jihar Taraba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp