Home Labarai ‘Yan Bindiga Sun Binne Ma’aikacin Poly Bayan Sun Karbi Miliyan 4

‘Yan Bindiga Sun Binne Ma’aikacin Poly Bayan Sun Karbi Miliyan 4

‘Yan bindiga sun hallaka ma’aikacin makarantar Polytechnic ta Talata-Mafara a jihar Zamfara Sanusi Halliru bayan sun karbi kudin fansar sa Naira miliyan 4.

‘Yan ta’addan sun yi garkuwa dashi ne akan hanyar Abuja zuwa Kaduna inda yake kokarin zuwa wajen wani taron karawa juna sani kafin yiwa kasa hidima.

Sun bukaci a biya naira miliyan 4 a matsayin kudin fansa, sai dai ba’a biya su kudin akan lokacin ba hakan ta sanya su halaka shi tare da binne gawar a cikin daji,

Wani makusanci mamacin, Muhammad Nasir, yace bayan sun tara miliyan Hudun sun kira ‘yan bindigar domin su fadi inda zasu kawo musu kudin su fanshi dan uwan su.

“Shugaban ‘yan bindigar ya fada mana lokaci da kuma wanda zai zo domin karbar kudin”. Amm da muka isa wajen bamu iske kowa ba.

“Sai daga bisani muka hangi wasu mutane saman Babura, da zuwan su suka bukaci mu basu kudin.

“Mun kuma mmika kudin gare su, said ai guda cikin su yace mana tuni dan uwan mu ya mutu.

“Mun bukaci su bamu gawar domin yi masa sutura kamar yadda Addini ya tanada, amma ga mamakin mu sai suka ce ai ya dade da mutuwa don haka sun binne shi.

“Sannan suka juya hankali kwance suka koma inda suka fito, Nasir ya bayyana hakan cikin bakin ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp