Home Labarai Hukumar da ke Sanya Ido A Kan Kafafen Yada Labarai Ta Kwace...

Hukumar da ke Sanya Ido A Kan Kafafen Yada Labarai Ta Kwace Lasisin AIT, Silverbird Da FM

Hukumar da ke sanya ido a kan kafafen watsa labaran Najeriya, National Broadcasting Commission (NBC) ta kwace lasisin wasu kafafen watsa labarai saboda gaza sabunta shi.

A wata sanarwa da shugaban hukumar, Malam Balarabe Shehu Illela, ya fitar ranar Juma’a ya ce kafafen watsa labaran da aka kwace lasisinsu sun hada da Silverbird TV, AIT, Raypower FM, Rhythm FM da karin wasu da dama bisa gaza biyan kudin da suka kai N2.66 bn don sabunta lasisin nasu.

Sanarwar ta ce an dauki matakin ne bayan an wallafa jerin kafafen watsa labarai da ba su sabunta lasisinsu ba.

A cewar hukumar, an bai wa kafofin watsa labaran karin makonnin biyu a watan Mayu domin su sabunta lasisinsu ko kuma su fuskanci yiwuwar saoke su amma suka ki.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp