Home Labarai An Ceto Wasu Cikin Wadanda Gini Ya Ruftawa a Kano –...

An Ceto Wasu Cikin Wadanda Gini Ya Ruftawa a Kano – Gwamnatin Jihar

Gwamnatin jihar Kano ta bada tabbacin ceto wasu mutane cikin wadanda gini ya rufta kan su a jihar dake Arewacin.

Mataimakin Gwamnan jihar Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ne ya bayyana hakan yayin da yakai ziyarar gani da ido wurin da lamarin ya faru, a kasuwar sayar da waya wayoyin hannu dake titin Beirut a jihar dake Arewacin Nijeriya.

Gwamnatin jihar ta bakin mataimakin gwamnan ta nuna kaduwar ta kan iftila’in, tare da jan hankalin Al’ummar da suka je wajen kallo dasu gaggauta barin wajen domin bawa masu aikin damar ceto wadanda ke karkashin gini, daga bisani ya jajantawa wadanda lamarin ya rutsa dasu.

Tun da fari dai an ruwaito cewa ginin ya ruf ta kan mutanen ne a yammacin wannan rana wanda kuma yanzu haka ana aikin ceto mutanen da suka makale.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp