Goyon Bayan PDP Nasara a 2023, Jihadi ne – Dan Takarar Gwamnan Katsina

Goyon Bayan PDP Nasara a 2023, Jihadi ne – Dan Takarar Gwamnan Katsina

 

SIYASA – Dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Katsina a zaben 2023, Sanata Yakubu Lado Danmarke, ya ce goyon bayan jam’iyyarsa ta lashe zabe ya wuce siyasa, yana mai cewa ” jihadi ne “. .

Lado ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Katsina lokacin da ya karbi bakuncin wasu jam’iyyun siyasa da suka koma PDP a karamar hukumar Safana ta jihar.

Ya kuma bayyana kwarin gwiwarsa na cewa da tarin masu sauya sheka a jihar, zai lashe zaben da gagarumin rinjaye.

“A nan Katsina, ba mu da rarrabuwar kawuna a PDP. Na yi takara da wasu uku, amma duk muna tare yanzu. Daya daga cikinsu shi ne abokin takarara a yanzu, dayan kuma yana neman kujerar majalisar tarayya.

“Na karshe kuma, koyaushe yana tare da mu, kuma duk abin da muke yi, muna tuntubar shi kuma yana ba da shawara mai mahimmanci,” in ji shi.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 33 minutes 48 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 15 minutes 13 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com