Home SIYASA Goyon Bayan PDP Nasara a 2023, Jihadi ne – Dan Takarar Gwamnan...

Goyon Bayan PDP Nasara a 2023, Jihadi ne – Dan Takarar Gwamnan Katsina

Goyon Bayan PDP Nasara a 2023, Jihadi ne – Dan Takarar Gwamnan Katsina

 

SIYASA – Dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Katsina a zaben 2023, Sanata Yakubu Lado Danmarke, ya ce goyon bayan jam’iyyarsa ta lashe zabe ya wuce siyasa, yana mai cewa ” jihadi ne “. .

Lado ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Katsina lokacin da ya karbi bakuncin wasu jam’iyyun siyasa da suka koma PDP a karamar hukumar Safana ta jihar.

Ya kuma bayyana kwarin gwiwarsa na cewa da tarin masu sauya sheka a jihar, zai lashe zaben da gagarumin rinjaye.

“A nan Katsina, ba mu da rarrabuwar kawuna a PDP. Na yi takara da wasu uku, amma duk muna tare yanzu. Daya daga cikinsu shi ne abokin takarara a yanzu, dayan kuma yana neman kujerar majalisar tarayya.

“Na karshe kuma, koyaushe yana tare da mu, kuma duk abin da muke yi, muna tuntubar shi kuma yana ba da shawara mai mahimmanci,” in ji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp