Home Labarai Ambaliyar Ruwa ta Shafi Yara 75,000 a Najeriya da Niger

Ambaliyar Ruwa ta Shafi Yara 75,000 a Najeriya da Niger

Ambaliyar Ruwa ta Shafi Yara 75,000 a Najeriya da Niger

 

By Gaggawa Digest-Satumba 16, 2022

Kungiyar Save the Children International (SCI) ta ce kimanin kananan yara 75,000 ne ambaliyar ruwa ta shafa a Nijar da Najeriya a makonnin da suka gabata.

A cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, ta ce sama da mutane 150,000 ne abin ya shafa ya bar al’umma da dama cikin rudani.

Sanarwar ta ce ambaliyar ta yi barna a yankunan Maradi, Zinder, Tillaberi da Tahoua na Nijar, da kuma jihohin Borno, Yobe, da Adamawa a Najeriya inda mutane sama da 100,000 suka shafa a Nijar kadai.

Shugabar kungiyar agaji ta Save the Children a Najeriya, Famari Barro, ta ce yana da matukar muhimmanci a samar da taimako ga mutanen da abin ya shafa musamman kananan yara, wadanda a kodayaushe suka fi shiga cikin mawuyacin hali.

Ya ce, “Yara na bukatar kwanciyar hankali, kuma muna bukatar mu tabbatar da cewa yara za su iya komawa makaranta a kwanaki masu zuwa. Yana da mahimmanci cewa akwai azuzuwa kuma amintacce ga yara kuma iyalai za su iya komawa gidajensu lafiya. ”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp