Home SIYASA Wike da Masu Ruwa da Tsaki na PDP Sun yi Taro

Wike da Masu Ruwa da Tsaki na PDP Sun yi Taro

Wike

Wike da Masu Ruwa da Tsaki na PDP Sun yi Taro

 

SIYASA – Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya kira taron shugabanni da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP a jihar.

Taron dai shi ne na farko a jihar tun bayan zaben fidda gwani na shugaban kasa da kuma rikicin da ya biyo bayan sakamakon ta.

Ko da yake ba a iya gano ajandar taron ba, wata majiya ta shaida wa wakilin PUNCH cewa tun bayan abubuwan da suka faru a jam’iyyar a matakin kasa har yanzu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a jihar ba su ji ta bakin gwamnan ba.

Don haka ana sa ran masu ruwa da tsaki za su ji ta bakin gwamnan kai tsaye kan matsayinsa da kuma matakin da za a dauka na gaba dangane da rikicin PDP.

Wadanda ake sa ran a taron sun hada da shugabannin jam’iyyar, ‘yan majalisar zartarwa na jiha, shugabannin kananan hukumomin jam’iyyar da sauran zababbun wasu.

Majiyar ta ce taron mai muhimmanci yana da nasaba da rikicin da ya barke a jam’iyyar a kwanakin baya, domin gwamnan zai yi wa mutanensa bayanin matsayin da tawagarsa ta dauka na ficewa daga majalisar yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar.

Wannan na zuwa ne gabanin wani taron manema labarai da aka shirya yi a safiyar Juma’a 23 ga watan Satumba, 2022, wanda Gwamna Wike zai yi jawabi a gidan gwamnati dake Fatakwal.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp