Home SIYASA Wike da Masu Ruwa da Tsaki na PDP Sun yi Taro

Wike da Masu Ruwa da Tsaki na PDP Sun yi Taro

Wike

Wike da Masu Ruwa da Tsaki na PDP Sun yi Taro

 

SIYASA – Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya kira taron shugabanni da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP a jihar.

Taron dai shi ne na farko a jihar tun bayan zaben fidda gwani na shugaban kasa da kuma rikicin da ya biyo bayan sakamakon ta.

Ko da yake ba a iya gano ajandar taron ba, wata majiya ta shaida wa wakilin PUNCH cewa tun bayan abubuwan da suka faru a jam’iyyar a matakin kasa har yanzu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a jihar ba su ji ta bakin gwamnan ba.

Don haka ana sa ran masu ruwa da tsaki za su ji ta bakin gwamnan kai tsaye kan matsayinsa da kuma matakin da za a dauka na gaba dangane da rikicin PDP.

Wadanda ake sa ran a taron sun hada da shugabannin jam’iyyar, ‘yan majalisar zartarwa na jiha, shugabannin kananan hukumomin jam’iyyar da sauran zababbun wasu.

Majiyar ta ce taron mai muhimmanci yana da nasaba da rikicin da ya barke a jam’iyyar a kwanakin baya, domin gwamnan zai yi wa mutanensa bayanin matsayin da tawagarsa ta dauka na ficewa daga majalisar yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar.

Wannan na zuwa ne gabanin wani taron manema labarai da aka shirya yi a safiyar Juma’a 23 ga watan Satumba, 2022, wanda Gwamna Wike zai yi jawabi a gidan gwamnati dake Fatakwal.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp