Home SIYASA Allah ya yi wa Mai Garin Lokoja Rasuwa

Allah ya yi wa Mai Garin Lokoja Rasuwa

Allah ya yi wa Mai Garin Lokoja Rasuwa

 

LABARIN SIYASA – An bayar da rahoton rasuwar basaraken gargajiyar Lokoja, wanda aka fi sani da Mai Gari na Lokoja, Alhaji Muhammadu Kabiru Makarfi III.

Majiyoyin fadar da dama sun shaidawa SIYASA DIGEST a daren Laraba cewa mai martaba sarkin ya rasu da misalin karfe 4 na yamma.

Wakilinmu ya kuma tattaro cewa basaraken mai shekaru 80 a duniya ya rasu ne a wani asibitin Abuja da ba a bayyana ba.

Mai Gari ya kwashe watanni yana jinya inda aka kai Asibitoci daban-daban a Saudiyya da Masar kafin daga bisani ya kare a Abuja.

Majiyoyin da suka kware a fadar sun kara da cewa za a yi jana’izarsa kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a ranar Alhamis.

Mai Gari ya hau karagar mulki tun 1991. Ya rasu ya bar mata da ‘ya’ya da jikoki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp