Allah ya yi wa Mai Garin Lokoja Rasuwa

Allah ya yi wa Mai Garin Lokoja Rasuwa

 

LABARIN SIYASA – An bayar da rahoton rasuwar basaraken gargajiyar Lokoja, wanda aka fi sani da Mai Gari na Lokoja, Alhaji Muhammadu Kabiru Makarfi III.

Majiyoyin fadar da dama sun shaidawa SIYASA DIGEST a daren Laraba cewa mai martaba sarkin ya rasu da misalin karfe 4 na yamma.

Wakilinmu ya kuma tattaro cewa basaraken mai shekaru 80 a duniya ya rasu ne a wani asibitin Abuja da ba a bayyana ba.

Mai Gari ya kwashe watanni yana jinya inda aka kai Asibitoci daban-daban a Saudiyya da Masar kafin daga bisani ya kare a Abuja.

Majiyoyin da suka kware a fadar sun kara da cewa za a yi jana’izarsa kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a ranar Alhamis.

Mai Gari ya hau karagar mulki tun 1991. Ya rasu ya bar mata da ‘ya’ya da jikoki.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 14 hours 43 minutes 6 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 16 hours 24 minutes 31 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com