Home SIYASA Allah ya yi wa Mai Garin Lokoja Rasuwa

Allah ya yi wa Mai Garin Lokoja Rasuwa

Allah ya yi wa Mai Garin Lokoja Rasuwa

 

LABARIN SIYASA – An bayar da rahoton rasuwar basaraken gargajiyar Lokoja, wanda aka fi sani da Mai Gari na Lokoja, Alhaji Muhammadu Kabiru Makarfi III.

Majiyoyin fadar da dama sun shaidawa SIYASA DIGEST a daren Laraba cewa mai martaba sarkin ya rasu da misalin karfe 4 na yamma.

Wakilinmu ya kuma tattaro cewa basaraken mai shekaru 80 a duniya ya rasu ne a wani asibitin Abuja da ba a bayyana ba.

Mai Gari ya kwashe watanni yana jinya inda aka kai Asibitoci daban-daban a Saudiyya da Masar kafin daga bisani ya kare a Abuja.

Majiyoyin da suka kware a fadar sun kara da cewa za a yi jana’izarsa kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a ranar Alhamis.

Mai Gari ya hau karagar mulki tun 1991. Ya rasu ya bar mata da ‘ya’ya da jikoki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp