Home SIYASA Tinubu ba ya Nan Yayin Da ‘Yan Takarar Shugaban Kasa sun Shirya...

Tinubu ba ya Nan Yayin Da ‘Yan Takarar Shugaban Kasa sun Shirya Sa Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya

Tinubu ba ya Nan Yayin Da ‘Yan Takarar Shugaban Kasa sun Shirya Sa Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya

 

SIYASA – Wasu ‘yan takarar shugaban kasa da shugabannin jam’iyyun siyasa 18 da suka yi wa rajista sun fara isa cibiyar taron kasa da kasa (ICC) domin rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya ta kasa gabanin babban zabe na 2023.

Kwamitin zaman lafiya na kasa karkashin jagorancin tsohon shugaban kasa Janar Abdulsalami Abubakar da Bishop Matthew Hassan Kukah ne suka shirya taron.

An kirkiro shirin ne a shekarar 2014 domin mayar da martani ga barazanar da ke kunno kai a babban zaben shekarar 2015.

‘Yan takarar da suka halarci bikin da ake shirin farawa sun hada da dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) Sanata Kashim Shettima wanda ke wakiltar abokin takararsa, Bola Ahmed Tinubu; ‘Yan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Action Alliance (AA) Omoleye Sowore da takwaransa na jam’iyyar New Nigerian Peoples Party (NNPP), Sanata Rabiu Kwanwaso.

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullah Adamu, shi ma yana kan kujerar domin gudanar da taron.

Cikakkun bayanai anjima…

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp