Home General ‘Yan Bindiga: An Ceto Sauran Fasinjojin Jirgin Kaduna zuwa Abuja da Suka...

‘Yan Bindiga: An Ceto Sauran Fasinjojin Jirgin Kaduna zuwa Abuja da Suka Rage Hannun ‘Yan Fashin Daji

Rahotanni daga Nijeriya na bayyana cewa An sako dukkan fasinjojin da suka rage a hannun wadanda ke garkuwa da su bayan da aka sace su a watan Maris na shekarar 2022 a cikin wani jirgin kasan da ke kan hanyar zuwa Kaduna daga birnin tarayya Abuja.
Wannan dai na kunshe ta cikin wata sanarwa da gwamnatin kasar ta fitar ta hannun sakataren wani kwamitin ma’aikatar tsaron Najeriya CDSAC Farfesa Usman Yusuf ya fitar a ranar ranar Laraba, wadda take da yammacin ranar laraba dakarun soji sun sami nasarar ce sauran mutane da suka rage hannun masu garkuwar.
“Ina mai farin cikin sanar da kasa da ma duniya cewa da misalin karfe 4 na yammacin yau Laraba 5 ga watan Oktoba 2022, kwamitin mutum bakwai da hafsan hafsoshin dakarun tsaron kasa Janar L. E. O. Irabor ya sami nasarar ceto sauran fasinjoji 23 da suka rage a hannun ‘yan ta’adda na Boko Haram bayan da suka kai hari kan jirgin kasan da ya taso daga Abuja zuwa Kaduna ranar 28 ga watan Maris na 2022.
Sanarwar ta kara da cewa, “Wannan kasar na cike da godiya ga sojojin Najeriya a karkashin jagorancin hafsan hafsoshin sojojin kasar, wanda shi ne ya jagoranci aikin daga farkonsa har zuwa karshe. Haka ma, sauran hukumomin tsaro da ma’aikatar sufuri duka sun taimaka gaya wajen nasarar da muka samu a wannan aikin.”
Sai dai kawo yanzu babu rahotannin inda aka kai fasinjojin da aka sako, ko yadda aka iya karbo su daga hannun ‘yan Boko Haram din da suka yi garkuwa da su na tsawon fiye da wata shida.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp