Home General Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Hallaka Mayakan ISWAP 19 a Jihar Borno

Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Hallaka Mayakan ISWAP 19 a Jihar Borno

Dakarun sojojin Nijeriya sun sami Nasarar hallaka mayakan boko haram tsagin ISWAP guda 19 tare da kame guda 73 a arewa maso gabashin kasar.

Wannan na kunshe ne ta ckin wata takardar sanarwa da aka rabawa manema labarai mai dauke da sa hannun darakatan yada labaran rundunar sojin Nijeriya Manjo Janar Musa Danmadami,dake dauke da kwanan watan 6 ga watan Oktoban 2022.

Sanarwar tace tsakanin 22 ga watan Satumba zuwa 4 ga watan Oktoban wannan shekara dakarun sojin Operation Hadin kai yayin da suke gudanar da ikin wazan da zaman lafiya a  kauyukan, tsunuka, da kuma biranen dake yakin arewa maso gabashin Nijeriya, dakarun sun gabatar da atisayen fatattakar mayakan a kananan hukumomin Biu, Damboa, kaga, Kukawa da Gubio duk a jihar Borno.

A yayin harin da dakarun sojojin suka kai sun sami nasara kame masu safarar kaya ga mayakan boko haram da na ISWAP, inda suka sami nasarar kwato kayayyaki da suka hadar da buhu 50 na busasshen Kifi, Buhu 2 na Busasshen Nama, sai kuma jarakuna 55 makare da man Fetir, buhu 1 na gwayi, sai buhu 13 na buredi, buhu wake guda 1, katan 5 na Omon wanke, 3 fakiti 3 na Batiri, sai jaka 50 ta maganin sauro, wayoyin salula 10, sai abun hawa guda 4, keke guda 1. Gami da zunzurutun kudi har naira miliyan 2 da dubu dari 479 da dari 740 da (2,479,740.00) gami da wasu kayyakin amfani.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp