Home General Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Hallaka Mayakan ISWAP 19 a Jihar Borno

Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Hallaka Mayakan ISWAP 19 a Jihar Borno

Dakarun sojojin Nijeriya sun sami Nasarar hallaka mayakan boko haram tsagin ISWAP guda 19 tare da kame guda 73 a arewa maso gabashin kasar.

Wannan na kunshe ne ta ckin wata takardar sanarwa da aka rabawa manema labarai mai dauke da sa hannun darakatan yada labaran rundunar sojin Nijeriya Manjo Janar Musa Danmadami,dake dauke da kwanan watan 6 ga watan Oktoban 2022.

Sanarwar tace tsakanin 22 ga watan Satumba zuwa 4 ga watan Oktoban wannan shekara dakarun sojin Operation Hadin kai yayin da suke gudanar da ikin wazan da zaman lafiya a  kauyukan, tsunuka, da kuma biranen dake yakin arewa maso gabashin Nijeriya, dakarun sun gabatar da atisayen fatattakar mayakan a kananan hukumomin Biu, Damboa, kaga, Kukawa da Gubio duk a jihar Borno.

A yayin harin da dakarun sojojin suka kai sun sami nasara kame masu safarar kaya ga mayakan boko haram da na ISWAP, inda suka sami nasarar kwato kayayyaki da suka hadar da buhu 50 na busasshen Kifi, Buhu 2 na Busasshen Nama, sai kuma jarakuna 55 makare da man Fetir, buhu 1 na gwayi, sai buhu 13 na buredi, buhu wake guda 1, katan 5 na Omon wanke, 3 fakiti 3 na Batiri, sai jaka 50 ta maganin sauro, wayoyin salula 10, sai abun hawa guda 4, keke guda 1. Gami da zunzurutun kudi har naira miliyan 2 da dubu dari 479 da dari 740 da (2,479,740.00) gami da wasu kayyakin amfani.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp