Home Labarai ASUU Na Shirin Janye Yajin Aiki Ranar Juma’a

ASUU Na Shirin Janye Yajin Aiki Ranar Juma’a

Alamu masu karfi na nuni da cewa yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta kwashe kusan shekara guda ta shiga zai kawo karshe a karshen mako.

Hakan ya biyo bayan kyakkyawan sakamako da aka samu a zaman da kungiyar ta yi da majalisar wakilai karkashin jagorancin Hon Femi Gbajabiamila.

Gbajabiamila da shugaban kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke, a ganawarsu ta karshe da sun ce “Za a kawo karshen yajin aikin nan da kwanaki” sannan kuma ya ce “akwai gagarumar nasara bayan lokacin da aka dauka ana cikin halin yajin aikin.

Yanzu haka dai majiyoyi daga ASUU sun bayyanawa cewa idan al’amura suka tafi kamar yadda aka tsara a wannan makon, za a yi sanarwar kawo karshen yajin aikin na tsawon watanni 8 ko kuma kafin Juma’a.

Yayin da ake sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari zai bayyana matakin karshe na gwamnati bisa shawarwarin Gbajabiamila a ranar Talata, shugabannin kungiyar ASUU na shiyya-shiyya kuma suna yin taro don duba cancantar shawarwarin da shugaban majalisar ya bayar wanda ake ganin ya tilastawa bangarorin biyu yin dabaru.

A cikin jadawalin ayyukan da majiyoyin suka rabawa manema labarai, kungiyar za ta gudanar da wani taro a  Laraba domin mayar da martani kan jawabin da shugaba Buhari ya yi a ranar Talata.

Majalisar za ta yi la’akari da shawarar da shugaban kasa ya yanke da kuma rangwamen da ya dace don kawo karshen yajin aikin.

A bisa ka’ida, babbar kungiyar ASUU ta yanke shawara, wato kwamitin zartarwa na kasa, NEC, zai yi zama a ranar Alhamis don yanke shawara kan ra’ayoyin da aka tattara daga tarukan farko.

A cewar majiyoyin, idan taron hukumar ya tsawaita har zuwa yammacin ranar Alhamis, za a sanar da matakin karshe a ranar Juma’a.

“Idan abubuwa suka tafi yadda aka tsara, tsakanin Alhamis zuwa Juma’a a janye yajin aikin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp