Home Labarai ASUU Na Shirin Janye Yajin Aiki Ranar Juma’a

ASUU Na Shirin Janye Yajin Aiki Ranar Juma’a

Alamu masu karfi na nuni da cewa yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta kwashe kusan shekara guda ta shiga zai kawo karshe a karshen mako.

Hakan ya biyo bayan kyakkyawan sakamako da aka samu a zaman da kungiyar ta yi da majalisar wakilai karkashin jagorancin Hon Femi Gbajabiamila.

Gbajabiamila da shugaban kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke, a ganawarsu ta karshe da sun ce “Za a kawo karshen yajin aikin nan da kwanaki” sannan kuma ya ce “akwai gagarumar nasara bayan lokacin da aka dauka ana cikin halin yajin aikin.

Yanzu haka dai majiyoyi daga ASUU sun bayyanawa cewa idan al’amura suka tafi kamar yadda aka tsara a wannan makon, za a yi sanarwar kawo karshen yajin aikin na tsawon watanni 8 ko kuma kafin Juma’a.

Yayin da ake sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari zai bayyana matakin karshe na gwamnati bisa shawarwarin Gbajabiamila a ranar Talata, shugabannin kungiyar ASUU na shiyya-shiyya kuma suna yin taro don duba cancantar shawarwarin da shugaban majalisar ya bayar wanda ake ganin ya tilastawa bangarorin biyu yin dabaru.

A cikin jadawalin ayyukan da majiyoyin suka rabawa manema labarai, kungiyar za ta gudanar da wani taro a  Laraba domin mayar da martani kan jawabin da shugaba Buhari ya yi a ranar Talata.

Majalisar za ta yi la’akari da shawarar da shugaban kasa ya yanke da kuma rangwamen da ya dace don kawo karshen yajin aikin.

A bisa ka’ida, babbar kungiyar ASUU ta yanke shawara, wato kwamitin zartarwa na kasa, NEC, zai yi zama a ranar Alhamis don yanke shawara kan ra’ayoyin da aka tattara daga tarukan farko.

A cewar majiyoyin, idan taron hukumar ya tsawaita har zuwa yammacin ranar Alhamis, za a sanar da matakin karshe a ranar Juma’a.

“Idan abubuwa suka tafi yadda aka tsara, tsakanin Alhamis zuwa Juma’a a janye yajin aikin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp