Home Labarai Kotu tace Jam’iyyar APC Bata da Dan Takarar Gwamna a jihar Adamawa

Kotu tace Jam’iyyar APC Bata da Dan Takarar Gwamna a jihar Adamawa

Binani

Wata Babbar kotun tarayya da ke zaman ta a Yola ta soke zaɓen fitar da ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC a jihar Adamawa, wanda Sanata A’isha Binani ta sami nasara.

A hukuncin da ta yanke, mai shari’a A.M Anka ta buƙaci Aisha Binani ta daina bayyana kanta a matsayin ƴar takarar gwamna a zaɓen gwamna na shekara ta 2023.

Kotun ta ce zaɓen ya zama haramtacce saboda aringizon ƙuri’a da kuma kawo wakilai daga ƙaramar hukumar Lamurde, inda ba a gudanar da zaɓen cikin gida na jam’iyyar ba.

Tsohon shugaban Hukumar Yaƙi da rashawa da yi wa tattalin arzikin Najeriya zagon ƙasa (EFCC) Mallam Nuhu Ribadu ne ya shigar da ƙarar, inda ya buƙaci kotu ta soke zaɓen, wanda aka gudanar a watan Maris.

Inda ya yi zargin an yi aringizon ƙuri’u, da sayen ƙuri’a da kuma bai wa daliget cin hanci.

Yanzu haka kotun ta ce jam’iyyar APC ba ta da ɗan takarar gwamna a jihar ta Adamawa a zaben shekara ta 2023.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp