Home Labarai An Kama Jami’an NIMC da Ake Zargi da Yin Rijistar ‘Yan Kasashen...

An Kama Jami’an NIMC da Ake Zargi da Yin Rijistar ‘Yan Kasashen Waje a Jamhuriyar Nijar

An Kama Jami’an NIMC da Ake Zargi da Yin Rijistar ‘Yan Kasashen Waje a Jamhuriyar Nijar

 

Jami’an rundunar sojin Najeriya da ke yankin yammacin Afirka a Jamhuriyar Nijar sun kama wasu jami’an hukumar jabu guda biyu da ake zargi da yi wa wasu ‘yan kasashen waje rijistar NIN.

Daraktan yada labarai na rundunar, Manjo Janar Musa Danmadami ne ya bayyana hakan a yayin taron tattaunawa na mako biyu a hedikwatar tsaro.

Janar Danmadami ya bayyana cewa wadanda ake zargin sun ziyarci sansanin ‘yan gudun hijira na Gagamari da ke jamhuriyar Nijar ne domin yin rijistar wadanda ba ‘yan Najeriya ba a sansanin ‘yan gudun hijirar, inda ya ce an kwato kayayyaki daga hannun wadanda ake zargin da suka hada da na’urar rajista ta kasa (NIN), na’urar bugu, na’urar laminating, na’urar bin diddigin kwamfuta da saitin janareta a tsakanin sauran abubuwa.

Janar din sojan ya kara da cewa sojojin sun kuma kama ‘yan ta’adda, masu samar da kayan aiki tare da kubutar da fararen hula a lokacin da suke gudanar da aikinsu.

A cewarsa, an mika su ga hukumar da ta dace domin daukar mataki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp