Home Labarai An Kama Jami’an NIMC da Ake Zargi da Yin Rijistar ‘Yan Kasashen...

An Kama Jami’an NIMC da Ake Zargi da Yin Rijistar ‘Yan Kasashen Waje a Jamhuriyar Nijar

An Kama Jami’an NIMC da Ake Zargi da Yin Rijistar ‘Yan Kasashen Waje a Jamhuriyar Nijar

 

Jami’an rundunar sojin Najeriya da ke yankin yammacin Afirka a Jamhuriyar Nijar sun kama wasu jami’an hukumar jabu guda biyu da ake zargi da yi wa wasu ‘yan kasashen waje rijistar NIN.

Daraktan yada labarai na rundunar, Manjo Janar Musa Danmadami ne ya bayyana hakan a yayin taron tattaunawa na mako biyu a hedikwatar tsaro.

Janar Danmadami ya bayyana cewa wadanda ake zargin sun ziyarci sansanin ‘yan gudun hijira na Gagamari da ke jamhuriyar Nijar ne domin yin rijistar wadanda ba ‘yan Najeriya ba a sansanin ‘yan gudun hijirar, inda ya ce an kwato kayayyaki daga hannun wadanda ake zargin da suka hada da na’urar rajista ta kasa (NIN), na’urar bugu, na’urar laminating, na’urar bin diddigin kwamfuta da saitin janareta a tsakanin sauran abubuwa.

Janar din sojan ya kara da cewa sojojin sun kuma kama ‘yan ta’adda, masu samar da kayan aiki tare da kubutar da fararen hula a lokacin da suke gudanar da aikinsu.

A cewarsa, an mika su ga hukumar da ta dace domin daukar mataki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp