Home Labarai ‘Yan Bindiga sun Sace Matafiya a Yankin Ekiti

‘Yan Bindiga sun Sace Matafiya a Yankin Ekiti

‘Yan Bindiga sun Sace Matafiya a Yankin Ekiti

 

Wasu ‘yan bindiga kimanin bakwai sun kai hari a kan titin Irele Ekiti, a karamar hukumar Ajoni da ke jihar Ekiti, inda suka yi awon gaba da matafiya hudu zuwa inda ba a san inda suke ba.

Majiyoyi sun ce matafiya hudun na kan hanyar zuwa birnin Ibadan na jihar Oyo ne da misalin karfe 11 na safiyar ranar Lahadi daga jihar Kogi inda suka halarci wani taron da lamarin ya faru.

Majiyar ta ce masu garkuwa da mutane dauke da bindigu sun bindige matafiyan ne a kofar Irele Ekiti da ke karshen Irele-OkeAko na hanyar inda suka garzaya da su dajin.

Wata majiya ta ce a ranar Litinin, “Ba mu ji komai daga bakin ‘yan bindigar ba tun ranar Lahadi. Muna fatan za su tuntubi iyalansu domin neman kudin fansa.”

Wani shugaban al’ummar Irele-Ekiti, wanda ya bayyana sunansa da Kehinde, ya tabbatar da sace shi.

Ya koka da yadda ‘yan bindiga ke kai hare-hare a yankin, inda ya yi kira ga gwamnati da ta kara kaimi wajen tabbatar da tsaro a yankin.

Kehinde ya bukaci gwamnan jihar Ekiti, Biodun Oyebanji, da ya ja hankalin sojoji da su samar da sansanin tsaro da za su kare yankin daga ‘yan bindigar da suka addabi yankin.

Kwamandan rundunar na Amotekun, Birgediya Janar Joe Komolafe (mai ritaya), wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce, “Rundunar jami’an tsaron na toshe dajin da ke yankin domin kubutar da wadanda lamarin ya rutsa da su tare da damke masu laifin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp