Gwamnatin Tarayya ta Tabbatar da Tsige Shugaban Hukumar Hidimar Kasa (NYSC)

Rahotannin na bayyana cewa ministan matasa da wasannin na Nijeriya Sunday Dare ya tabbatar da tsige darakta janar na hukumar yi wa kasa hidima (NYSC birgidiya janar Muhammad Fadah

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa a daren juma’a domin tabbatar da sakon tambayar da aka yi masa kan gaskiyar labarin.

Tunda fari da jaridar PRNigeria ta ruwaito cewa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya sallami Shugaban Hukumar kula da Matasa Ƴan yi wa ƙasa Hidima, NYSC, Muhammad Kukah Fadah, ƙasa da watanni 6 da naɗa shi.

Kawo yanzu dai babu wani dalili da a ka bayyana cewa shi ne ya sanya Buhari ya sallami Fadah, amma wata nahiyar sirri a fadar shugaban ƙasa ta shaida wa jaridar PRNigeria cewa korar ta sa ba ta rasa nasaba da rashin ƙoƙari tun bayan da ya kama aiki.

Sai dai kuma PRNigeria ta ruwaito cewa tuni a ka baiwa Fadah umarnin ya mika ragamar aiki ga ma’aikaci mafi matsayi a hukumar wanda zai zama shugaban na riƙo.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 16 hours 26 minutes 52 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 18 hours 8 minutes 17 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com