Home Labarai Jami’ai a Afrika ta kudu sun tabbatar da hallaka mutane da yawansu...

Jami’ai a Afrika ta kudu sun tabbatar da hallaka mutane da yawansu ya haura Dubu 7 a sassan Kasar,

Wasu sabbin alkaluma da rundunar ‘yan sandan Afrika ta kudu ta fitar sun nuna yadda aka kashe mutanen da yawansu ya haura dubu 7 a sassan kasar, wanda ke nuna karuwar laifuka da tashe-tashen hankula a kasar.

Rahoton da rundunar ‘yan sandan ta mikawa kwamitin majalisar kasar mai kula da laifuka a jiya laraba, ya nuna yadda aikata laifuka ya kai kololuwa tsakanin 1 ga watan Yulin da ya gabata zuwa 30 ga watan Satumba.

Rahoton ‘yan sandan ya bayyana cewa an samu karuwar aikata laifuka da kashe-kashe da akalla kashi 14 idan akwa kwatanta da yawan mutanen da aka kashe a irin lokacin cikin shekarar da ta gabata.

A irin wannan lokaci cikin shekarar 2021 makamantan tashe-tashen hankulan da rikice rikice da kuma kashe-kashen babu gaira babu dalili ya kai ga mutuwar mutane dubu 6 da 163 adadin da bai kai yadda aka samu a bana ba.

Akalla mata dubu guda ke cikin wadanda aka kashe cikin watannin 3 a Afrika ta kudu yayinda aka ci zarafin matan da yawansu ya haura dubu 13 sai kuma wasu dubu 1 da 277 da aka nufaci kashe su amma suka kubuta da kyar.

Rahoton rundunar ‘yan sandan ya nuna yadda aka yi garkuwa da mutanen da yawansu ya haura dubu 4000 cikin watannin 3 alkaluman da ke nuna yadda laifukan garkuwa suka karu da fin kashi 100 idan an kwatanta da bara.

Haka zalika laifukan cin zarafin mata da yara ta hanyar fyade ya karu da kashi 11 inda yanzu haka ake da kararraki fiye da dubu 10 gaban kotuna kan irin wadannan laifuka a sassan kasar cikin wannan lokaci.

Rahoton ya kuma bayyana yadda aka kashe yaran da yawansu ya kai 550 daga watan Aprilu zuwa Satumban shekarar nan a kasar ta Afrika ta kudu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp