Home General ‘Yan sanda sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan da ake nema ruwa...

‘Yan sanda sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan da ake nema ruwa a jallo a jihar katsina

‘Yan sanda sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan da ake nema ruwa a jallo a jihar katsina,
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da kakakin rundunar SP GAMBO ISAH, ANIPR ya fita a madadin kwamishinan ‘yan sanda jihar, sanarwa tace ‘yan ta’addan sun hadar da Na-Iraqi, Na-Masari.
Sanarwa mai dauke da kwanan watan 13 ga watan Disambar 2022 tace da misalin karfe 7:30 jami’an ‘yansan sun sami kiran cewa ‘yan bindiga sun tasamma yankin Sokoto – Rima Quarters dake karamar hukumar Dutsinma a jihar Katsina suna harbi kan mai uwa da wabi da bindiga kirar AK47, da nufin yin garkuwa da wani mazaunin yankin.
Babu bata lokaci dakarun dake lura da yankin suka garzaya wurin domin kai dauki, da isar su suka fara musayar wuta da ‘yan bindigar suka kuma sami nasarar hallaka 2 daga cikin su wadanda kuma suna jadawalin wadanda ake nema ruwa a jallo da suka hadar da Abu Na-Iraqi da Abu Na-Masari suka kuma sami nasarar kwato bindiga kirar AK47.
Jami’an ‘Yan sanda sun shiga bincike domin gano wadan suka tsere da raunukan harbi a jikin su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp