Home General ‘Yan sanda sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan da ake nema ruwa...

‘Yan sanda sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan da ake nema ruwa a jallo a jihar katsina

‘Yan sanda sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan da ake nema ruwa a jallo a jihar katsina,
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da kakakin rundunar SP GAMBO ISAH, ANIPR ya fita a madadin kwamishinan ‘yan sanda jihar, sanarwa tace ‘yan ta’addan sun hadar da Na-Iraqi, Na-Masari.
Sanarwa mai dauke da kwanan watan 13 ga watan Disambar 2022 tace da misalin karfe 7:30 jami’an ‘yansan sun sami kiran cewa ‘yan bindiga sun tasamma yankin Sokoto – Rima Quarters dake karamar hukumar Dutsinma a jihar Katsina suna harbi kan mai uwa da wabi da bindiga kirar AK47, da nufin yin garkuwa da wani mazaunin yankin.
Babu bata lokaci dakarun dake lura da yankin suka garzaya wurin domin kai dauki, da isar su suka fara musayar wuta da ‘yan bindigar suka kuma sami nasarar hallaka 2 daga cikin su wadanda kuma suna jadawalin wadanda ake nema ruwa a jallo da suka hadar da Abu Na-Iraqi da Abu Na-Masari suka kuma sami nasarar kwato bindiga kirar AK47.
Jami’an ‘Yan sanda sun shiga bincike domin gano wadan suka tsere da raunukan harbi a jikin su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp