Babban kwamandan rundunar sojojin kasan Nijeriyar Laftanal Janar Faruk yahaya ya bukaci sabbin sojojin da suka kammala karatu a makarantar Horas da sojojin kasar ta NDA da suka hadar da sojin kasa dana sama da su hidimtawa kasar cikin girma da mutuntawa kasancewar su na sojoji.
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da Daraktan yada labarai na rundunar sojin Nijeriya birgediya Janal ONYEMA NWACHUKWU Ya fitar mai duke da kwanan watan 16 ga watan Disambar 2022. Ta Ambato COAS na gargadin a yayin da yake jawabi ga daliban da ke shirin kammala karatunsu a makarantar horasa da sojoji ta Nijeriya (NDA) dake Jihar kaduna Bayan kwashe watanni tara suna daukar horo.
Sama da dalibai 300 ne ki shirin kammala daukan horoN sojin kasa dana sama dake jiran Tabbatarwar Gwamnatin Tarayya Bayan kammala karatunsu a wani gagarumin faretin da za’a gudanar a NDA dake Kaduna a ranar Asabar 17 ga watan Disambar 2022.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1190 days 11 hours 54 minutes 14 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 35 minutes 39 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com