Dakarun sojin Saman Nijeriya sun Halaka ‘Ya Ta’adda sama da 60 a jihar Zamfara

Dakarun sojojin saman Najeriya sun yi luguden wuta da jirage kan sansanin ‘yan bindiga dake kauyen Mutumji a karamar hukumar Maru ta Jihar Zamfara, abinda yayi sanadiyar kashe hallaka akalla 60 daga cikinsu.

Rahotanni sun ce daga cikin mutanen da harin ya ritsa da su harda mata da kuma yara wadanda suke yankin lokacin da harin.

Bayanai sun ce harin ya biyo bayan koken da mazauna kauyukan Malele da Ruwan Tofa da ‘yan awaki suka gabatar na cewar ‘yan bindigar sun farwa garuruwansu, abinda ya sa sojojin daukar matakin kai musu dauki ta sama.

Wani mazaunin yankin ya tabbatar da aukuwar lamarin, yayin da ya kuma bayyana mana cewar yayin kai daukin ta sama sojojin cikin kuskure sun hallaka wasu daga cikin abokan aikin su dake kai hari ta kasa.

Majiyar tace yayin da ake wannan, wasu yan bindigar sun yiwa tawagar sojoji kwantar bauna inda suka kaiwa motocinsu guda 3 hari a yankin.

Jihar Zamfara na ci gaba da fuskantar munanan hare hare daga ‘yan bindiga wadanda ke sanyawa garuruwa haraji domin hana kai musu hari.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 42 minutes 38 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 24 minutes 3 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com