Home DUNIYA Sojojin Nijeriya na cigaba da samun Nasarar kan mayan Boko Haram a...

Sojojin Nijeriya na cigaba da samun Nasarar kan mayan Boko Haram a Arewa maso gabashin Kasar

Dakarun sojojin Nijeriya sun sami nasarar kama mayakan boko haram, tare da hallaka wasu a mafa
Rundunar sojojin nijeriya karkashin Dakarun operation hadin kai bisa hadin gwiwa da jami’an sa kai na vigilanti a daren litinin sun sami nasara hallaka mayakan boko haram 8 tare da kama guda a raye a wani harin kwanton bauna da suka gudanar a karamar hukumar Mafa dake jihar Borno a Arewa maso gabashin Nijeriya.
Wannan na zuwa ne bayan da hafsan hafsoshin Sojin Nijeriya Laftanal Janar Farouk Yahaya, ya bukaci dakarun sojin da su sake matsa kaimi wajen kai hare-hare ga ‘yan ta’addan dake cikin dajin Sambisa da kuma yankin tafkin Chadi.
Jaridar PRnigeria ta tattaro cewa dakarun sojin sun sami nasarar kai harin kwanton baunar ne bayan wasu bayanan sirri da suka samu a kauyen Ngoum dake kusa da garin Maiduguri babban birnin jihar ta Borno, hakan ya basu damar fatattakar mayakan.
‘yan ta’addan da dakarun suka hallaka sune wadanda ke aikata fashi da makami a dukkan fadin kananan hukumomin Mafa, jere da kunduga
Dakarun sun sami nasarar halaka 8 daga cikin su tare da kama guda 1 da raia, sai kuma nasarar kwato baburan hawa da kuma bindiga kirar AK47 a cewa PRNigeria.
Haka kuma a wani cigaban wata kungiya daga cikin Al’ummar kauyen kwayam a jihar borno sun sami nasarar halaka wasu ‘yan ta’adda da ake kyautata zaton mayan boko haram ne, a wani harin kwanton bauna da suka gudanar da makamin kwari da baka.
Majiyoyin sun kuma tabbatar da cewa matasan kauyen sun sami nasarar kwato babur din hawa guda daya inda suka mika shi ga hannun dakarun sojojin dake Gwongulan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp