Home General Tunubu alkawarin bunkasa tsaro da harkokin tattalin arzikin jihar kano idan ya...

Tunubu alkawarin bunkasa tsaro da harkokin tattalin arzikin jihar kano idan ya sami nasara

Dan takarar shugabancin Nijeriya na jam’iyyar APC Asiwaju Bola Ahmad Tinubu ya yi alkawarin bunkasa tsaro da harkokin tattalin arzikin jihar kano idan ya sami nasara.

Tinubu ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da malaman Arewa maso yammacin Nigeria a jihar Kano.

Yace kasancewar kano cibiyar Arewacin Nigeria akwai bukatar a bata kulawa ta musamman saboda idan ta bunkasa dukkanin jihohin Arewacin Nigeria sun bunkasa.

Bola Tinubu ya kuma yi alkawarin samar da wani tsari da zai taimaka wajen inganta harkokin karatun al-qur’ani saboda magance matsalar barace-barace a kasar.

Ya kuma yi alkawarin baiwa malamai dama a gwamnatin tarayya ta yadda za’a dama da su domin inganta kasar. Tinubu ya bukaci Malamai da su umarci dalibansu da sauran magoya bayansu da su zabe shi saboda yafi dukkanin yan takarar shugaban kasa chanchanta.

Da yake nasa jawabin gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya ƙalubalanci masu ganin baiken jam’iyyar APC don ta haɗa yan takarar shugaban kasa duk Musulmi, Inda yace haɗa Musulmi da Musulmi a takarar shugaban kasa ba sabon Abu bane a Ƙasar Nijeriyar .

Ganduje ya kuma bada tabbacin cewa al’ummar Nigeria suna son jam’iyyar APC da yan takarar su Kuma zasu zabe su a babban zaben Mai zuwa .

Malamai da dama ne dai suka halarci taron ganawar  wadanda suka fito daga jihohin Arewacin Nigeria domin halartar taron wanda ke cikin jerin tarukan da aka tsara don yakin neman zaben Tinubu a kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp